Trump Ya Bayyana Ra’ayin Tura Falasdinawan Gaza Zuwa Masar Ko Jordan
Published: 26th, January 2025 GMT
Shugaban Amurka Donald Trump ya zayyana wani ra’ayi mai manufar tsarkake zirin Gaza.
Trump na mai cewa yana son aikewa da Falasdinawa daga yankin zuwa kasashen Masar da Jordan “na dan lokaci” ko kuma “a cikin dogon lokaci”. don samun zaman lafiya.
Ana dai ganin tamakar Trump na kwatanta yankin Falasdinu da “wurin rushewa nan gaba” bayan watanni 15 na yakin da Isra’ila ta kadamar kan Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
News Fox: Sau 6 Yemen Ta Kakkabo Jiragen Amurka Samfurin Mq 9 A Karkashin Gwamnatin Trump
Tashar talbijin din “News Fox” ta kasar Amurka mai ra’ayin ‘yan mazan jiya ta watsa wani rahoto da yake cewa; Daga lokacin da Donald Trump ya zama shugaban kasa, sau 6 sojojin Yemen su ka kakkabo jiragen sama maras matuki samfurin Mq9.
Rahoton na tashar talabijin din Fox ya kuma yi ishara da yadda sojojin na Yemen su ka kakkabo jirgin sama marasa matuki da marecen juma’a, wanda shi ne karo na 6 tun daga ranar 3 ga watan Maris.
Rahoton ya kuma kara da cewa; Kowane daya daga cikin jiragen sama marasa matuki samfurin mq9 ya kai dalar Amurka miliyan 30.
Bugu da kari rahoton ya kuma bayyana cewa; Sau 35 sojojin Amurka suna kai wa kasar Yemen hare-hare, amma kuma duk da haka har yanzu sojojin Yemen suna ci gaba da kai wa wadannan jiragen na Amurka masu tsada hari. Haka nan kuma sojojin na Yemen suna ci gaba da hana wucewar jiragen ruwa da suke zuwa HKI.
Wannan rahoton kuma ya yi ishara da yadda sojojin na Yemen suke kai wa HKI hare-hare da makamai masu linzami masu cin dogon zango.
Daga fara kai farmakin Aksa zuwa yanzu, adadin jiragen Amurka samfurin MQ 9 da sojojin yemen su ka kakkabo sun kai 16, sai dai wata majiyar ta bayyana cewa, jiragen da sojojin na Yemen su ka kakkabo sun kai 20. Wani jami’in ma’aikatar tsaro ta kasar Amurka ya sanar da tashar talbijin din ta Fox cewa; A 2024 Amurka ta kera, jragen MQ 9 guda 230, amma a kasar Yemen kadai an harbo 16 daga cikinsu.