Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-31@12:50:34 GMT

Ofishin UNICEF Na Kano Ya Ziyarci Majalisar Dokokin Jihar Jigawa

Published: 26th, January 2025 GMT

Ofishin UNICEF Na Kano Ya Ziyarci Majalisar Dokokin Jihar Jigawa

Majalisar dokokin jihar Jigawa ta jaddada aniyar ta na hada kai da ofishin kula da kananan yara na majalisar dinkin duniya UNICEF domin samun nasarar aiwatar da tsare-tsare da za su inganta rayuwar yara da marasa galihu a jihar.

 

Mataimakin kakakin majalisar, Alhaji Sani Isyaku Abubakar, ya bada wannan tabbacin lokacin da ya karbi bakuncin tawagar ofishin UNICEF na Kano karkashin jagorancin Hajiya Fatima Adamu.

 

Ya lura cewa irin wannan haɗin gwiwa tsakanin majalisa, Action Against Hunger da Save the Children International sun haifar da sakamako mai kyau ta hanyar tallafawa matakan majalisa ta hanyar fasaha da ba da shawara don tsara manufofin da sauran tsare-tsaren a Jigawa.

 

Alhaji Sani Isyaku Abubakar ya bada tabbacin ci gaba da kulla alaka da hukumar UNICEF domin tabbatar da jin dadin masu karamin karfi ta hanyar kafa hukumar kare al’umma da za ta jagoranci aiwatar da manufofin.

 

Tun da farko shugabar tawagar Kano ta ofishin UNICEF Hajiya Fatima Adamu, ta bayyana cewa sun kai ziyarar ne domin neman karin goyon baya da hadin kan ‘yan majalisa domin aiwatar da manufofin kare al’umma da kuma gangamin rage yawan fitar yara daga makaranta a jihar Jigawa.

 

KARSHE/USMAN MZ/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Edo Za Ta Binciki Kisan Matafiya ‘Yan Arewa A Jihar

Sakataren yaɗa labaran gwamnan, Fred Itua, ya bayyana cewa waɗanda aka kashe sun fito daga Fatakwal, a Jihar Ribas, amma ‘yan banga sun ɗauka cewa ‘yan ta’adda ne.

Gwamna Okpebholo ya kai ziyara wajen da lamarin ya faru, inda ya jaddada cewa za a gudanar da bincike mai zurfi domin hukunta masu hannu a kisan.

Amnesty International da tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, sun yi kira da a tabbatar da an yi adalci.

Gwamnan Edo ya yaba wa shugabannin Arewa bisa yadda suka kwantar da hankula tare da guje wa ɗaukar fansa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
  • Kashe Matafiya: Gwamnatin Kano Ta Aika Tawaga Zuwa Edo
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Fiji: Ya Kamata A Koyi Fasahohin Da Kasar Sin Ta Samu A Fannin Raya Kasa
  • Siriya : Ofishin jakadancin Amurka ya yi gargadi game da yiyuwar hare-hare a yayin bikin sallah
  • Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah
  • Wadanda Iftila’in Tankar Mai Ya Sha A Jigawa Sun Sami Naira Miliyan 4 Kowannensu
  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Kisan ’yan Arewa a Edo ya tayar da ƙura
  • Gwamnatin Edo Za Ta Binciki Kisan Matafiya ‘Yan Arewa A Jihar
  • ’Yan sanda sun haramta hawan Sallah a Kano