Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya ce kusan yara miliyan 5.4 ‘yan kasa da shekaru biyar a yankin arewa maso yamma da arewa maso gabas na fama da matsananciyar rashin abinci mai gina jiki, inda aka yi hasashen za a samu Karin masu wannan matsala su miliyan daya nan da watan Afrilun 2025.

 

Wakiliyar UNICEF a Najeriya Ms Cristian Munduate ta bayyana hakan a wani taron manema labarai kan rikicin da ya addabi miliyoyin yara a jihar Zamfara da kuma fadin Najeriya da aka gudanar a Gusau babban birnin jihar Zamfara.

 

Ms Munduate wadda ta yi tsokaci kan halin da kananan yara ke ciki a Zamfara, ta ce jihar na da yara miliyan 1.2 kuma daga cikin adadin yara 250,000 ne ke fama da matsananciyar rashin abinci mai gina jiki (SAM).

 

A cewarta, don magance matsananciyar wahalar da ake fama da ita a fadin Najeriya, ciki har da Sokoto, Zamfara, da Katsina, ta bukaci sama da dala miliyan 250.

 

Ta kuma bayyana cewa, UNICEF na da niyyar kula da yara 400,000 ‘yan kasa da shekaru 5 da ke fama da matsananciyar rashin abinci mai gina jiki yayin da karin yara 200,000 a yankin arewa maso yamma za su bukaci Shirye-shiryen Abinci a 2025 idan aka kwatanta da 2024.

 

“Sama da yara 300,000 a Sokoto da Zamfara na bukatar rigakafin cutar kyanda”

 

Domin magance kalubalen yadda ya kamata, wakiliyar UNICEF ta bukaci gwamnatoci a dukkan matakai da su fadada ayyukan kiwon lafiya da karfafa shirye-shiryen kiwon lafiyar al’umma.

 

Ta kara da cewa, lamarin yana bukatar daukar matakin gaggawa, da hada kai, da kuma jajircewa wajen ceto rayuka, da maido da fata, da gina kyakkyawar makoma ga yaran Zamfara da sauran su.

 

 

COV/AMINU DALHATU/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya

Saɓanin shekarun baya, azumin watan Ramadan na bana ya zo a daidai lokacin da rahotanni ke nuna cewa farashin kayan abinci na sauka a sassan Najeriya.

Kayayyakin masarufi irinsu shinkafa da wake da fulawa na daga cikin waɗanda aka fi sarrafawa a watan na Ramadan, kuma su ne masu gwaggwaɓan kaso a faɗuwar farashin.

Farashin kayan masarufi na sauka a wannan karo ne baya kimanin shekara biyu a jere suna tashi a ƙasar.

Haka kuma, ana iya cewa ’yan Najeriya sun saba ganin tashin farashin kaya, musamman na abinci, a gabnin watan Ramadan.

Duk da mutane suna nuna jin daɗinsu da saukar farashin a wannan karon, amma wasu na cewa hakan bai kawo sauƙi ga talaka ba, a wannan lokaci da aka ɗauki haramar ibadar azumi, saboda rashin kuɗi a hannun jama’a.

An ga watan Ramadan a Najeriya An kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano

Wata matar aure da Aminiya ta zanta da ita ta ce, duk saukar da farashin abinci ke yi, amma ta hatsi ake yi ba ta kayan marmari ba

Ƙarancin masu sayayya

A zagayen da Aminiya ta gudanar a Kasuwar Rimi da ke Kano, ta lura da ƙarancin masu zuwa cefanen azumi a satin jajiberan Ramadan, saɓanin lokutan baya.

Bisa al’ada dai, mata kan yi cefanen kayan abinci na musamman da ake amfani da su a watan azumi, a wasu lokutan ma, har da sabbin mazuban abin ci da sha ga mai gida.

Jiya ta fi yau

Fatima Muhammad Nasir matar aure ce mai ’ya’ya biyu a Kano, ta kuma bayyana wa Aminiya cewa a kowacce shekara idan ta zo gara bara da bana ake a kan farashin kayan abinci a Najeriya.

“A bangarena kayan abincin da suka fi muhimmanci a watan azumi su ne dankali, mai, fulawa, doya, kayan shayi, da aya, zoɓo, wake, gyadar kunu, da sauransu.

Yanzu ta hatsi ake…

“A shekarun baya ina da ƙarfin sayen su nama, kaji, kifi, da doya, da ƙwai amma a bana sai wane da wane.

“Yanzu ta hatsi ake yi ba waɗannan ba. Na baki misali shekaru biyu baya kajin da mai gidan ke saya a kan N7,000 – N11,000 a bana N25,000 zuwa N30,000 ne.

“Gyaɗar kunu a kan N5,000 muka saya kwano ɗaya, aya N1,300, Zoɓo kuma N1,000. Rabin buhun dankali shekaru biyu baya akan N10,000 ne, amma yanzu akan N30,000 ake sayar da shi.”

Ita ma Asma’u Muhammad cewa ta yi tsadar kayan abinci a bana ba kaɗan ba ne idan aka kwatanta da azumin bara.

“Akwai abubuwan da sayen su sai ka ci ka tada kai a yanzu saɓanin baya.

A da, masu girke-girke a soshiyal midiya na yin girkin da muke kallo mu kwaikwaya mu yi a namu gidan, amma yanzu ba komai ne zai yi wu ba.

Ƙalubale

Wata matsala da a azumin bara aka dinga kuka da ita ce ta tsadar ƙanƙara ba da ma ƙarancinta, inda aka dinga sayen manya a kan N500 zuwa sama, ƙanana kuma N300.

Asma’u ta ce babbar matsalar da ke kawo hakan ba ta wuce matsalar rashin wutar lantarki da ta ƙi ci taƙi cinyewa ba, amma a bana tana fatan za a samu sauyi.

“Ƙalubalen da muka fuskanta a bara shi ne tsadar ƙanƙara da rashin wuta. Mutane sun sha wahala saboda an yi rana sosai kuma sanyin da za ka sha an tsuga masa kuɗi. Amma ina fata a bana haka ba za ta faru ba.”

Ita ma Fatima ta bayyana rashin wutar a matsayin babban ƙalubale, musamman a lokutan buɗa baki da sahur.

“Haka muka dinga sahur da buɗa baki a duhu a bara, saboda rashin wuta. Allah Ya sa a bana ba haka za a yi ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya
  • MDD Ta Bayyana Cewa Yara Fiye Da 100,000 Ne Suka Ka Yi Rijistan Fara Karatu A Makarantun Gaza Na Sabuwar Shekarar Karatu
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Nabamamu a Zamfara
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara
  • Kebbi Ta Kashe Naira miliyan 67 Wajen Biya Sadakin Ma’aurata 300
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar Jiki
  • Sojojin Nijeriya Za Su Fara Karɓar N3,000 Kudin Abinci A Rana
  • NAFDAC Ta Kaddamar Da Sabbin Shirye-Shiryen Yaki Da Jaribun Magunguna
  • Gidauniyar Sarki Salman Ta Rab Tallafin Abinci Ga Mutane 2,450 A Kebbi
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Biya Diyar Sama Da N1.5 Biliyan Ga Wadanda Aikin Tituna Ya Shafa