Hukumar Kula Da Taswira Ta Jihar Kebbi (KEBGIS), ta tsara wani gagarumin shiri na samar da kudaden shiga na sama da Naira biliyan daya a shekarar 2025.

 

Babban Manajan Hukumar, Bashiru Saidu Bakuwai, wanda ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a kan tabbatar da nadinsa a matsayin babban Manaja, ya ce hakan ya nuna kwazon hukumar a karkashin ma’aikatar filaye da gidaje na tallafa wa tattalin arzikin jihar.

 

Malam Saidu Bakuwai, ya ba da karin haske kan ayyukan hukumar da suka hada da alhakin duk wasu takardu da suka shafi filaye, tsarawa da bayar da takaddun kowane gida, sake tantancewa, daidaitawa, da kuma tsarin rajistar kadarorin.

 

Sauran su ne Gudanarwa da Rajista na ma’amalar filaye, gami da Ayyuka, jinginar gida, Canjin manufa (amfani da ƙasa), haɗaka da rabe-rabe tare da tabbatar da ingantaccen tsarin gudanar da filaye daidai da mafi kyawun ayyuka na duniya.

 

Da yake mika godiyarsa ga Kwamared Nasir Idris da ya jagoranci gwamnatin bisa yadda take tantance daidaikun mutane bisa cancanta da kwazo, don basu mukamai, Saidu Bakuwai, ya ba da tabbacin hukumarsa za ta himmatu wajen rubanya kokari wajen bayar da gudunmawar ci gaban manufofin gwamnatin na inganta shugabanci nagari, da inganta ayyuka. da haɓaka kudaden shiga na cikin gida a jihar.

 

Sai dai ya yi kira ga takwarorinsa da aka tabbatar da su a sassa daban-daban da su ba da goyon bayansu ga gwamnatin Kwamared Nasir Idris domin su hada kai wajen ba da damar gudanar da ayyukansu na daidaiku da na gamayya don tabbatar da samun nasarar jagoranci.

 

COV/Abdullahi Tukur/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin Saudiyya ya haɗa kai da gwamnatin Jigawa kan noman dabino

Samar da dabino zai samu sauyi mai mahimmanci a Jihar Jigawa bayan da wani kamfani daga kasar Saudiyya mai samar da dabino da gwamnatin jihar suka ƙulla yarjejeniya domin ƙara yawan amfanin gona.

Ta wannan haɗin gwiwa za a kawo sababbin fasahohin zamani da irin dabino masu yawa don shigar da su cikin tsarin noma.

Sanata Natasha na neman diyyar N100bn wurin Akpabio Ƙungiya ta rage farashin kayan marmari saboda Azumin Ramadan

A cewar bayanai daga Hukumar Abinci da Aikin Noma ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO), Saudiyya ita ce ƙasa ta biyu mafi girma wajen samar da dabino na duniya, inda take samar da tan miliyan 1.61 na dabino.

Masar ita ce ƙasa mafi girma wajen samar da dabino, inda ta noma tan miliyan 1.73 na dabino a shekarar 2022, yayin da Aljeriya ke matsayi na uku da tan miliyan 1.25.

Haɗin gwiwar Gwamnatin Jihar Jigawa da wannan rukunin daga Saudiyya tare da Netay Agro-Tech, wani kamfanin amfani da ke Nijeriya ma gudanar da harkokin noma, zai kawo karuwar samuwar dabino a jihar.

Kasar Nijeriya na samar da kusan tan 21,000 na dabino a kowace shekara, inda Jihar Jigawa ke cikin jihohi mafi girma wajen samar da dabino.

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, yayin da yake jawabi lokacin da ya karɓi wata tawaga daga babban kamfanin noma na Saudiyya, wanda ya ƙware wajen shuka dabino da sarrafa gonaki a ofishinsa da ke Dutse, ya ce wannan haɗin gwiwa zai kawo sabon salo ga samar da dabino a Jigawa.

Gwamnan ya bayyana goyon bayan gwamnatinsa ga wannan yunƙuri, yana mai cewa ya dace da ajandar bunkasa aikin gona ta jihar.

“Mun yi maraba da zuwanku Jihar Jigawa tare da nuna godiya ga sha’awar da kuka nuna wajen yin aiki tare da mu.

“A matsayinmu na gwamnati, mun jajirce kan wannan haɗin gwiwa saboda zai amfani al’ummarmu sosai.

“Zuwanku da sha’awar yin haɗin gwiwa da mu wajen kafa gonakin dabino a fadin jihar, da kuma inganta samar da alkama, sun yi daidai da burinmu na bunkasa aikin noma,” in ji gwamnan.

Ya sake jaddada shirinsa na samar da dukkan kayan aiki da ake bukata don tabbatar da nasarar aiwatar da wannan shiri.

Ya bayyana kwarin gwiwa cewa, haɗin gwiwar zai samar da fa’idodi masu ban mamaki tare da mayar da Jigawa ta zama jagora a masana’antar dabino ta duniya.

Shugaban tawagar, Abdul’aziz Abdurrahman-Al-Awf ya jaddada ƙudurinsu na kawo fasahohin noma na zamani zuwa Jihar Jigawa.

“Muna son tabbatar da samar da dabino a duk shekara, ba wai kawai a wasu yanayi ba, kuma haɗin gwiwarmu zai haɗa da horar da manoma da ba wa matasa dama,” in ji shi.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano
  • Wata Mujalla Ta Zabi Shugaban NPA A Matsayin Gwarzonta Na Shekarar 2025
  • NAHCON Ta Naɗa Sabon Sakatare
  • Kebbi Ta Kashe Naira miliyan 67 Wajen Biya Sadakin Ma’aurata 300
  • Gwamnatin Kano Za Ta Ɗau Nauyin Ɗalibai 1,002 Domin Karatu A Ƙasashen Waje
  • Sin Ta Gabatar Da Ka’idar Sarrafa Mutum-Mutumin Inji Mai Kula Da Tsoffi Na Duniya
  • Gidauniyar Sarki Salman Ta Rab Tallafin Abinci Ga Mutane 2,450 A Kebbi
  • Gwamna Namadi Ya Nada Jami’an Alhazai 27 Tare Da Kara Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajji
  • Kamfanin Saudiyya ya haɗa kai da gwamnatin Jigawa kan noman dabino
  • Ahmed Musa ya buƙaci a gudanar da bincike kan mutuwar ɗan wasan Nijeriya a Uganda