Gwamnatin Jihar Jigawa ta yaba da kokarin ‘yan Nigeria mazauna kasar Saudiyya bisa gudunmawar da suke bayarwa ga harkokin kiwon lafiyar al’ummar jihar.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan a lokacin rangadin duba aikin idanu da ‘yan Nigeria mazauna kasar Saudiyya da hadin gwiwar gwamnatin jihar ke gudanarwa a babban asibitin Dutse.

Gwamnan wanda ya zagaya wuraren da aka kwantar da wadanda aka yi wa aikin idanun, ya nuna jin dadinsa da gamsuwa da yawan mutanen da aka yi wa aikin.

Daga cikin wadanda suka amfana da aikin sun hada da masu matsalar ido su 500 da aka yi wa tiyata, sai kuma mutane  300 da aka baiwa

gilashi.

Kazalika, mutane 400 kuma suka sami maganin ciwon ido.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara

Rundunar ’yan sandan Jihar Zamfara ta kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ake kira Ɗan Mudale da ya addabi mazauna yankin Tsafe da kewaye.

Rundunar ta ce a jiya Alhamis ne ta daƙile wani harin ’yan bindiga a ƙauyen Keta da ke Ƙaramar Hukumar Tsafe ta jihar.

’Yan sanda sun haramta hawan Sallah a Kano Ɓarayin kekunan ɗinki sun shiga hannu a Borno

Hakan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Yazid Abubakar ya fitar a Gusau, babban birnin jihar.

A cewar DSP Yazid, a yayin daƙile harin ne ’yan sanda suka kashe gomman ’yan bindigar ciki har da Ɗan Mudale wanda ya addabi al’ummar yankin.

Ya ce rundunar haɗin gwiwa da ta haɗa da ’yan sanda da askarawa da kuma mafarauta ce ta yi karon batta da ’yan ta’addar da aka riƙa musayar wuta.

Sai dai ya bayyana takaicin cewa wani jami’in ɗan sanda daya da askarawa huɗu da kuma mafarauta sun bayar da ransu a yayin artabun.

Sanarwar ta ce a halin yanzu wasu mafarauta biyu na karɓar magani a Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Gusau.

Kazalika, rundunar ’yan sandan ta ƙara jaddada ƙudirinta na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

Ta yi kira ga mazauna da su riƙa gaggauta miƙa mata rahoton duk wani motsi da su aminta da shi ba domin a ɗauki matakin da ya dace.

Mutuwar Ɗan Mudale ne zuwa bayan kashe Kachalla Isuhu Yellow, wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ke sahun waɗanda suka jagoranci kitsa harin da aka kai jirgin ƙasan Kaduna zuwa Abuja shekaru biyu da suka gabata.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Umar Namadi Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Sallah Karama
  • Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Hamas ta yi Tir da kakkausar murya da harin Isra’ila kan masu aikin ceto a Gaza
  • Wadanda Iftila’in Tankar Mai Ya Sha A Jigawa Sun Sami Naira Miliyan 4 Kowannensu
  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • Sharhi: Taruka Da Gangamin Ranar Quds Ta Duniya 2025
  • Kisan ’yan Arewa a Edo ya tayar da ƙura
  • An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara