An Jinjinawa Gwamnatin Jigawa Bisa Bunkasa Ilimin ‘Ya’ya Mata
Published: 26th, January 2025 GMT
Kungiyar kwamishinonin kudi ta kasa ta jinjinawa kokarin gwamnatin jihar Jigawa na bunkasa Ilmin ya’ya mata.
Shugaban kungiyar kuma kwamishinan kudi na jihar Ekiti, Mr Akim Oyebode ya bayyana hakan a lokacin da suka ziyarci Gwamna Umar Namadi a gidan gwamnati dake Dutse.
Mr Akim Oyebode ya ce kungiyar tana alfahari da ayyukan raya kasa da Gwamna Umar Namadi ya aiwatar tun hawansa karagar mulki, a sassan jihar ta Jigawan.
Yana mai cewar sun ziyarci jihar Jigawa ne domin yi wa Gwamnan ta’aziyyar rashin da aka masa.
A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi ya yaba musu bisa wannan ziyara tare da fatan za su koma jihohinsu lafiya.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
Jami’an tsaro a tarayyar Najeriya a birnin Kano sun haramta daban da aka saba yi a karshen watan azumi a birnin.
Jaridar Premium times ta Najeriya ta nakalto Jami’an tsaron kasar suna bada wannan sanarwan ne bayan da sarki na 15 Wato Aminu- Ado Bayero ya bada sanarwan janye daban da ya shirya gabatarwa a kwanakin salla Karamah.
Shugaban Jami’an tsaron ya bayyana haka ne a wani taron yan jarida da ya gabatar a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa baza su amince da gudanar da taron Durba a karamar sallah a wannan shekara ba.
Kakakin yansada na jihar Kano Haruna Kiyawa, ya sanya sanarwan a shafinsa na Facebook.
Kafin haka aranar 18 ga watan Maris da muke ciki ne gwamna Abba Yusuf na Jihar Kano ya umurce masarautar Kano ta shirin gudanar da wannan bikin kamar yadda ta saba. Ya gwamnatinsa ba zata amincewa masu adawa su kawo cikas a cikin shirin ba.
Gwamnan ya yi wa mutanen alkawali kan cewa Jami’an tsaro zasu tabbatar da tsaro da zaman lafiya a lokacin bikin Dubar, mai magana da yawan gwamnan jihar ya kara jaddadawa.
Sai da Mr Kiyawa ya bayyana cewa sun dauki makakin hana kilisa ko Durbar kwata-kwata a jihar ne bayan sun yi nazararin harkokin tsaro a jihar suka kuma ga cewa ba za su amince da duk abinda zai tada hankalin mutanen jihar ba.