Dan takarar zaben maye gurbin Dan Majalisar Tarayya da ke wakiltar Mazabar Chikum da Kajuru a jam’iyar APC Arc Sani A Abbas Sardaunan Chikum ya nada kwamitin mutane 7 domin raba tallafin karatu ga daliban yankin sa su 100 da suke karatun kimiyya da fasaha a manyan marantun Gwamnati.

Wannan wata manuniya ce game da kudurin Arc Sani Abbas na karfafa matasa ta bangaren ilimin don gobe su tayi kyau.

Babban aikin wannan kwamitin shi ne tantance daliban da suka cancanci amfana da wannan tallafin musamman wadanda babu ke barazanar hana su karatu. Wanda yin haka zai taimaka wajen tallafa musu su nemi ilimi don cike gibin da ake samu ta wannan bangaren.

Wannan tallafin kadan ne daga cikin irin manofofin da yake da su ba ga al’ummar sa ba, yana nuna cewa yana son ganin an sami al’umma mai ilimi.

‘Yan kwamitin sun hada da Hon. Dauda Abdulkadir Kujama a matsayin shugaba Sai wakilan kwamitin da suka hada da Hon Ibrahim Garba Danmajen Chikun da Hon. Ibrahim Umar.

Sauran su ne Mrs. Rebecca Akapson da Hon. Daniel Sisin Kobo

Saifu Adamu Bawa Kajuru sai Hon. Ganaka James Kogi da aka ba sakataren kwamitin.

 

Wanda ke bukatar samun wannan tallafi sai ya sauke wannan takarda ya cika ya kawo.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi

An shiga ruɗu da fargaba a garuruwan ƙasar Chadi da dama, sakamakon jita-jita da kafofin sada zumunta na yanar gizo ke yaɗawa cewa wasu matsafa na satar al’aurar maza.

Tun daga birnin Moundou da ke kudancin kasar da lamarin ya fara samun asali, inda wasu matasa hudu suka yi ikirarin cewa an sace musu al’aurarsu ta hanyar bakar tsafi, na yaduwa kamar wutar daji a wasu manyan biranen ƙasar Chadi.

Sakamakon jita-jita da bidiyoyi iri-iri da ake yadawa a shafukan sada zumunta, duk da cewa ba a tabbatar da wannan zargi a likitanci ko a hukumance ba, lamarin ya bazu tare da tada hankula har a tsakiyar N’Djamena, babban birnin kasar, inda wasu fusatattun mutane suka yi yunkurin kashe wani mutum wanda suka zarga da sace al’aurar wasu yara maza uku bayan ya yi musabaha da su, sai dai ya tsira da ransa sakamakon shiga tsakani da ’yan sanda suka yi, amma ya ji jiki da ɗan karen duka.

Babu tushe a zahiri

A yayin da ake fuskantar wannan al’amari wanda a halin yanzu girmansa na iya haifar da hargitsi na zaman lafiyar jama’a, gwamnati ta yanke shawarar tashi tsaye don ƙoƙarin kawo karshensa.

Kakakin gwamnatin Chadi, Gassim Cherrif ya ce lamarin na neman wuce gona da iri, domin kuwa ana kai wa mutane hari tare da jikkata da dama saboda zargi marasa tushe a zahari, yana mai cewa gwamnati ba za ta zuba ido tana gani har lamarin ya girma ba, ta yadda mutane ke ɗaukar doka da hannunsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan Almujtaba (a) 110
  • Makarantar Bare: Shekara 20 dalibai na karatu a matsanancin yanayi
  • Cibiyoyin Hada-Hadar Kudi Na Ketare Suna Da Kyakkyawar Fata Game Da Kasuwar Lamuni Ta Sin
  • Fursunoni 62 Sun Rubuta Jarrabawar NECO da MBAIS A Kano
  • Kwamitin Gudanar da Kasuwa Maras Shinge Ta Maigatari Sun Ziyarci Fadar Gumel
  • Bukatar Kawo Karshen Mamayar Da Kamaru Ke Yi Wa Yankunan Nijeriya
  • Matan da suka tsira daga Boko Haram na buƙatar tallafin musamman
  • AGILE: Gwamnatin Kaduna da Bankin Duniya Na Sauya Rayuwar ’Ya’ya Mata Ta Hanyar Ilimi
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta