Hukumar kula da gandun daji na Hadejia ta ce wuraren shakatawa na kasa suna taka rawar gani ta fuskar kiyaye halittu, da magance matsalolin sauyin yanayi, da inganta bincike, da ci gaba, gami da samar da ayyukan yi a Najeriya.

Mukaddashin jami’in kula da gandun dajin, Mista Jonah Moses ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar neman shawarwari ofishin wayar da kan jama’a na kasa da ke Dutse, babban birnin jihar Jigawa.

Ya nanata cewa al’umma za su kara fahimtar fa’idojin irin wadannan wurare ne kadai idan Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Kasa NOA, ta taimaka wajen fadakarwa ko ilmantar da jama’a.

Jonah Moses ya bayyana cewa, sun kawo ziyarar ce domin ganawa da masu ruwa da tsaki irin su hukumar ta NOA, wadanda za su iya taimakawa wajen fahimtar da jama’a game da gandun  daji na Hadejia.

Da yake mayar da martani, Daraktan Hukumar Wayar da Kan Jma’a ta kasa NOA na jihar Jigawa, Malam Ahmad Tijjani Ibrahim ya yabawa mai kula da gandun dajin na Hadejia da tawagarsa bisa da  kwazon da suke nuna wajen tafiyar da ayyukansu.

Ya kara da cewa hukumar ta ba da fifiko kan batun sauyin yanayi, inda ta samar da sashen kula da muhalli, da yanayi, da  makamashi.

Shugaban hukumar ta NOA ya tabbatar wa tawagar cewa a shirye hukumar ta ke na zaburar da al’ummar kasa game da ayyukan gandun dajin.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Sakon jagora ga shugaban kasar Rasha yana da alaka da ci gaban kasa da kasa da na yanki

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana hakan ne a yau Alhamis a birnin Moscow na kasar Rasha cewa: Abu ne da ya dace a rubuta sakon da Jagoran juyin juya halin Musulunci ya aikewa shugaban kasar Rasha dangane da ci gaban kasa da kasa da na yanki da kuma batutuwan da suka shafi kasashen biyu.

Araqchi ya bayyana hakan ne a lokacin da ya isa filin tashi da saukar jiragen sama na Vnukovo da ke birnin Moscow a yau, yayin da yake amsa tambayar da wakilin IRNA ya yi masa kan abubuwan da ke cikin sakon jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei zuwa ga shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya kara da cewa: Ziyarar tasa tana da manufofi daban-daban, yana mai bayanin cewa, tun da farko an shirya ziyarar ne domin isar da rubutaccen sako daga Jagoran juyin juya halin Musulunci ga shugaban kasar Rasha, kuma ta zo daidai da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan da kuma tattaunawa ta kai tsaye.

Ya kara da cewa, tun a baya, har ya zuwa yanzu, a ko da yaushe Iran tana gudanar da shawarwari na kut-da-kut da abokanta na kasar Rasha kan batun makamashin nukiliya, yana mai cewa, suna kuma tattaunawa da Rasha da China, kuma a yanzu da aka samu damar da ta dace, za a iya yin shawarwari tare da jami’an Rasha.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Yi Aiki Tare Don Daidaita Mummunan Yanayi A Yankin Manyan Tabkuna Na Afirka
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Maniyatan Bana A Jigawa
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa Ta Shirya Bitar Ga Malaman Bita na Kananan Hukumomi 27
  • Hukumar EFCC Ta Kama Mutane 40 da Ake Zargi da Damfarar Intanet
  • Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano
  • Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara
  • Majalisar Kaduna ta Amince da Kudirin Kula da Lafiyar Kwakwalwa na Jihar
  • Xi Ya Isa Kuala Lumpur Domin Ziyarar Aiki A Malaysia