Ambaliyar Ruwa Ta Haifar Da Koma-baya A Fannin Ilimi A Najeriya-UNICEF
Published: 26th, January 2025 GMT
Daga cikin yara ‘yan makaranta miliyan 242 da matsanancin yanayi ya raba da muhallansu a kasashe 85 a shekarar 2024, dalibai miliyan 2 da dubu 200 ne a Najeriya suka rabu da muhallansu, lamarin da ya kawo cikas ga harkokin ilimi a shekarar.
Rahoton wanda Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya fitar a daidai lokacin da duniya ke bikin ranar ilimi ta duniya ta shekarar 2025, ya nuna cewa a Najeriya baki daya dalibai miliyan 2,200,200 ne suka daina makaranta sakamakon ambaliyar ruwa.
Da take gabatar da jawabi kan tasirin da sauyin yanayi ke da shi ga ilimin yara, shugaban ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahama Farah ya bayyana cewa, ambaliyar ruwa da ta afku a jihar Jigawa a shekarar da ta gabata ta lalata gine-ginen makarantu 115, wanda hakan ya kawo cikas ga dalibai.
Ya bayyana alhininsa kan yadda lamarin ya haifar da tsawaita rufe makarantu, wanda ya shafi karatun yara sama da 92,518 a fadin kananan hukumomi 27 na jihar.
“A jihar Jigawa, ambaliyar ruwan da ta afku a shekarar da ta gabata ta lalata gine-gine da kayayyakin makarantu 115, wanda hakan ya sa ba za a iya amfani da su ba.
“Hakan ya haifar da tsawaita rufe makarantu da kuma rashin wadatar ilimi ga dalibai kimanin 92,518, wadanda 43,813 daga cikinsu mata ne, yayin da 48,705 kuma yara maza ne, a fadin kananan hukumomi 27 na jihar,” Mista Farah.
Ya yi nuni da cewa, UNICEF tare da tallafi daga ofishin kula da harkokin kasashen waje da na kungiyar kasashen renon Ingila da ke Burtaniya, na tallafa wa gwamnatocin jihohin Kano da Jigawa, don samar da yanayin koyo mai kyau domin rage tasirin sauyin yanayi da ya shafi koyon ilimia makarantu.
Ya bayyana cewa, a shekarar 2024, UNICEF ta dauki nauyin matasa dubu daya, wadanda 350 daga cikinsu sun fito ne daga jihar Jigawa, yayin da 650 kuma suka fito daga Katsina, don dasa bishiyu 300 a yankin hamada da kuma wuraren da ake fama da ambaliyar ruwa a jihohin biyu, domin dakile tasirin sauyin yanayi.
“Tare da goyon bayan abokan hulda da suka hada da ofishin kula da harkokin kasashen waje, da na kungiyar kasashen renon Ingila da ke Birtaniya, UNICEF na tallafawa jihohin Kano da Jigawa don samar da yanayin koyo mai kyau, don rage tasirin da sauyin yanayi ke haifarwa”.
Shugaban na UNICEF ya kuma bayyana cewa a shekarar da ta gabata asusun ya gina cibiyoyin kula da tsaftar ruwa da tsaftar muhalli (WASH) a makarantu da cibiyoyin kiwon lafiya a wuraren da ake bukata a cikin jihohin uku.
Ya ce asusun ya kuma gina tare da gyara wuraren tsaftar muhalli a makarantu 33, inda aka gina 25 a jihar Kano, sauran 8 kuma a jihar Jigawa, wadanda yara 39,432 ke amfani da su a jihohin biyu.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya
Saɓanin shekarun baya, azumin watan Ramadan na bana ya zo a daidai lokacin da rahotanni ke nuna cewa farashin kayan abinci na sauka a sassan Najeriya.
Kayayyakin masarufi irinsu shinkafa da wake da fulawa na daga cikin waɗanda aka fi sarrafawa a watan na Ramadan, kuma su ne masu gwaggwaɓan kaso a faɗuwar farashin.
Farashin kayan masarufi na sauka a wannan karo ne baya kimanin shekara biyu a jere suna tashi a ƙasar.
Haka kuma, ana iya cewa ’yan Najeriya sun saba ganin tashin farashin kaya, musamman na abinci, a gabnin watan Ramadan.
Duk da mutane suna nuna jin daɗinsu da saukar farashin a wannan karon, amma wasu na cewa hakan bai kawo sauƙi ga talaka ba, a wannan lokaci da aka ɗauki haramar ibadar azumi, saboda rashin kuɗi a hannun jama’a.
An ga watan Ramadan a Najeriya An kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a KanoWata matar aure da Aminiya ta zanta da ita ta ce, duk saukar da farashin abinci ke yi, amma ta hatsi ake yi ba ta kayan marmari ba
Ƙarancin masu sayayyaA zagayen da Aminiya ta gudanar a Kasuwar Rimi da ke Kano, ta lura da ƙarancin masu zuwa cefanen azumi a satin jajiberan Ramadan, saɓanin lokutan baya.
Bisa al’ada dai, mata kan yi cefanen kayan abinci na musamman da ake amfani da su a watan azumi, a wasu lokutan ma, har da sabbin mazuban abin ci da sha ga mai gida.
Jiya ta fi yauFatima Muhammad Nasir matar aure ce mai ’ya’ya biyu a Kano, ta kuma bayyana wa Aminiya cewa a kowacce shekara idan ta zo gara bara da bana ake a kan farashin kayan abinci a Najeriya.
“A bangarena kayan abincin da suka fi muhimmanci a watan azumi su ne dankali, mai, fulawa, doya, kayan shayi, da aya, zoɓo, wake, gyadar kunu, da sauransu.
Yanzu ta hatsi ake…“A shekarun baya ina da ƙarfin sayen su nama, kaji, kifi, da doya, da ƙwai amma a bana sai wane da wane.
“Yanzu ta hatsi ake yi ba waɗannan ba. Na baki misali shekaru biyu baya kajin da mai gidan ke saya a kan N7,000 – N11,000 a bana N25,000 zuwa N30,000 ne.
“Gyaɗar kunu a kan N5,000 muka saya kwano ɗaya, aya N1,300, Zoɓo kuma N1,000. Rabin buhun dankali shekaru biyu baya akan N10,000 ne, amma yanzu akan N30,000 ake sayar da shi.”
Ita ma Asma’u Muhammad cewa ta yi tsadar kayan abinci a bana ba kaɗan ba ne idan aka kwatanta da azumin bara.
“Akwai abubuwan da sayen su sai ka ci ka tada kai a yanzu saɓanin baya.
A da, masu girke-girke a soshiyal midiya na yin girkin da muke kallo mu kwaikwaya mu yi a namu gidan, amma yanzu ba komai ne zai yi wu ba.
ƘalubaleWata matsala da a azumin bara aka dinga kuka da ita ce ta tsadar ƙanƙara ba da ma ƙarancinta, inda aka dinga sayen manya a kan N500 zuwa sama, ƙanana kuma N300.
Asma’u ta ce babbar matsalar da ke kawo hakan ba ta wuce matsalar rashin wutar lantarki da ta ƙi ci taƙi cinyewa ba, amma a bana tana fatan za a samu sauyi.
“Ƙalubalen da muka fuskanta a bara shi ne tsadar ƙanƙara da rashin wuta. Mutane sun sha wahala saboda an yi rana sosai kuma sanyin da za ka sha an tsuga masa kuɗi. Amma ina fata a bana haka ba za ta faru ba.”
Ita ma Fatima ta bayyana rashin wutar a matsayin babban ƙalubale, musamman a lokutan buɗa baki da sahur.
“Haka muka dinga sahur da buɗa baki a duhu a bara, saboda rashin wuta. Allah Ya sa a bana ba haka za a yi ba.”