UNICEF Zai Shawo Matsalar Yawan Yara Da Ba Sa Zuwa Makaranta A Arewa Maso Yammacin Najeriya
Published: 26th, January 2025 GMT
Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya bukaci masu tsara manufofi a fannin ilimi a Najeriya da su dauki kwararan matakai don magance gibin da ke tattare da zamantakewa da al’adu da ababen more rayuwa da manufofin da ke haifar da yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a kasar.
Shugabar ofishin UNICEF na Kano, Rahama Rihood Farah, ne ya yi wannan kiran a wani taron manema labarai na bikin ranar ilimi ta duniya ta shekarar 2025.
Ya yi nuni da cewa, Jihohin Kano, da Jigawa da Katsina suna da adadin yara miliyandaya da dubu dari takwas da sittin da uku, da dari biyu da bakwai (1,863,207) da ba sa zuwa makaranta a matakin firamare, da kuma miliyan daya da dubu dari daya da saba’in da shidd, da dari tara da goma sha takwas(1,176,918), a matakin kananan makarantun sakandare, wanda ya bayyana a matsayin abin ban tsoro.
Ya gano wasu kalubalen da ke ci gaba da faruwa a halin da ake ciki baya ga makaranta, da suka hada da rashin isassun kudade, da rashin kula da al’adu, da rashin isassun kayayyakin more rayuwa a makarantu, da karancin ma’aikata da gudun hijira sakamakon ambaliyar ruwa da sauran illolin sauyin yanayi.
“Yayin da Arewa maso Yammacin Najeriya ta kasance ta biyu a kasar da ba a zuwa makaranta, lamarin da ake fama da shi a jihohin Kano da Jigawa da Katsina yana da ban tsoro.
“Abin da ya kara ta’azzara shi ne sakamakon rashin ingantaccen ilimi ga yaran da suka yi sa’ar shiga makaranta.
“A halin yanzu akwai kimanin yara miliyan goma da dari biyu a matakin firamare da ba sa zuwa makaranta a Najeriya, inda kashi 16 cikin 100 sun fito ne daga jihohin Kano, da Jigawa da Katsina, a cewar rahoton MICS na shekarar 2021.
“Kusan yara miliyan daya ne ba sa zuwa makaranta a jihar Kano da jimillar mutane 989,234, yayin da a Jigawa ana da jimillar 337,861 sai jihar Katsina da ke da yara 536,112 da ba sa zuwa makaranta.”
Mr Farah ya bukaci gwamnatocin jihohin Kano, da Jigawa da Katsina da su daidaita kasafin kudi tare da fitar da su a zahiri ga bangaren ilimi daidai da abin da ake bukata na Manufofin Ci Gaba Mai Dorewa na SDG da ma’aunin Hukumar kula da Ilimi, da Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO) don ingantacciyar sakamako a fannin.
Ya kuma yi kira ga gwamnatocin wadannan jahohin da su tunkari kalubalen samun ilimi ta hanyar fadada abubuwan more rayuwa a makarantu da daukar kwararrun malamai da shigar da makarantun kur’ani a cikin tsari na yau da kullun.
Daga Isma’il Adamu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai
Masarautar Kauru da ke jihar Kaduna ta jaddada kudirinta na tabbatar da tsaro, inda ta bukaci mazauna yankin da su kasance masu taka-tsan-tsan duk da ci gaban da gwamnati ta samu a baya-bayan nan wajen magance matsalar ‘yan fashi da garkuwa da mutane da kuma munanan hare-hare.
Mai martaba Sarkin Kauru, Alhaji Zakari Ya’u Usman na biyu, ya jaddada muhimmancin hadin kai wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro a lokacin da ya gabatar da sakon Sallar a fadarsa da ke Kauru.
Alhaji Zakari Ya’u Usman ya kuma yi gargadi game da masu ba da labari da ke taimaka wa masu laifi tare da karfafa gwiwar mazauna yankin da su kai rahoton duk wani abu da ake zargi.
Dangane da harkokin kiwon lafiya, Sarkin ya bukaci iyaye da su ba da fifiko ga allurar rigakafin yara don kare su daga cututtukan da za a iya rigakafin su.
Ya kuma shawarci mata masu juna biyu da su rika zuwa duba lafiyarsu akai-akai, sannan ya shawarci jama’a da su nemi kulawar lafiya a kan lokaci domin rage kamuwa da cututtuka kamar hawan jini da ciwon suga.
A cewarsa, Masarautar ta nuna godiya ga gwamnatin jihar kan aikin hanyar Pambeguwa zuwa Kauru da kuma tallafawa manoma ta hanyar rabon taki. Sai dai Sarkin ya roki a kara ayyukan hanyoyin da suka hada da Kauru zuwa Mariri a karamar hukumar Lere, Unguwan Ganye zuwa Dokan Karji mai hade da Kasuwan Magani a karamar hukumar Kauru, da kuma titin mai tsawon kilomita 10 a cikin garin Kauru.
Ya kuma bukaci a kammala kashi na biyu na gyaran fadar Kauru, musamman a wuraren da ke bukatar kulawar gaggawa, musamman a lokacin damina.
Sarkin ya yi addu’a don ci gaba da zaman lafiya da wadata a shekaru masu zuwa.
Hakazalika, Sakataren Masarautar, Malam Muhammad Sani Suleiman (Danburan Kauru) ya nuna jin dadinsa ga wadanda suka halarci bukukuwan Sallah tare da jajantawa iyalan wadanda rashin tsaro ya shafa.
COV/Yusuf Zubairu Kauru