Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-20@11:19:02 GMT

An Gudanar Da Taron WASA Na Rundunar Sojin Najeriya A Gusau

Published: 26th, January 2025 GMT

An Gudanar Da Taron WASA Na Rundunar Sojin Najeriya A Gusau

Kwamandan runduna ta 1 ta sojojin Najeriya da ke Gusau, Birgediya Janar Opurum Timothy, ya bayyana  wa al’ummar jihar Zamfara da ma kasa baki daya aniyar rundunar sojojin Najeriya na ci gaba da aiki tukuru domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a karshen taron wasannin rundunar sojojin Najeriya ta yammacin Afirka WASA 2024 da aka gudanar a Gusau.

Taro West African Social Activities WASA wani taro ne na shekara-shekara da rundunar sojojin Najeriya ke shiryawa domin  wasannin gargajiya na wannan  yankin na Afirka.

Taron na shekara-shekara yana tattaro Jami’ai, Sojoji, da iyalansu  cikin annashuwa domin wasannin al’adun da kuma bikin ƙarshen  shekara.

Janar Opurum wanda ya jaddada kudirin rundunar na kawar da ‘yan fashi da kuma dawo da zaman lafiya a Zamfara da yankin Arewa maso Yamma gaba daya, ya yi kira ga sojojin da su jajirce wajen gudanar da ayyukansu, yana mai jaddada cewa, sadaukarwarsu da  na da matukar muhimmanci wajen samun zaman lafiya mai dorewa.

Kwamandan Birgediya wanda ake yi wa lakabi da “Jar Kunama”, ya yabawa al’ummar Zamfara bisa yadda suke ba da hadin kai, musamman ta hanyar samar da muhimman bayanan sirri, wanda ya haifar da gagarumar nasara.

Tun da farko, Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara, wanda kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Meriga ya wakilta, ya yabawa rundunar sojojin Najeriya da sauran jami’an tsaro bisa namijin kokarin da suke yi na samar da zaman lafiya mai dorewa a fadin jihar ta Zamfara.

Taron WASA na bana a Gusau ya samu halartar manyan baki da suka hada da sarakunan gargajiya da shugabannin sauran hukumomin tsaro kamar rundunar sojojin saman Najeriya da jami’an tsaro da dai sauransu.

Muhimman abubuwan da suka faru a wajen taron sun hada da, baje kolin al’adu da raye-raye, wasan kokowa, da dai sauransu.

Yayin da wasu da dama da suka yi nasara suka je gida da kyaututtuka daban-daban da suka hada da man girki, shinkafa da sauran kyaututtuka.

Daga Aminu Dalhatu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue

Hukumomi a jihar Benue dake Najeriya sun ce adadin wadanda suka mutu  a harin da ‘yan bindiga suka kai a hukumomin Ukum da Kogo ya kai 56.

Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, a wata ziyara a yankin ya shaidawa manema labarai cewa  adadin wadanda suka mutu a harin ya kai 56.

”A yanzu, mutum 56 ne suka mutu wadanda ba su ji ba su gani ba, da suka hada da iyaye da maza da mata da kananan yara”, in ji shi.

Gwamnan ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta gaggauta daukar matakai domin kawo karshen hare-hare a jihar.

Gwamnan ya ce tuni gwamnatin jihar ta kara tura jami’an tsaro zuwa yankunan domin kwantar da hankula.

Harin na zuwa ne kimanin mako biyu bayan wasu yan bindiga sun kashe fiye da mutum 100 a wasu hare-hare a jihar Plateau mai makwabtaka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
  • An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar
  • ‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara
  • Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa
  • Rundunar ‘Yansanda Ta Tuhumi Jami’anta Da ‘Yan Kasar Sin Ke Raba Wa Kudi A Wani Bidiyo Da Ke Yawo
  • APC Ta Gaza Gudanar Da Taron NEC Cikin Shekaru Biyu – PDP Ta Zarge Su
  • Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta
  • Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista
  • BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano