Gwamnatin Jihar Jigawa ta yaba da shirin tallafawa al’umma da Shugaban karamar hukumar Sule Tankarkar ya bullo da shi a yankin.

Gwamnan Jihar, Mallam Umar Namadi ya bayyana haka a lokacin da ya halarci taron kaddamar da rabon tallafin da aka gudanar a karamar hukumar.

Malam Umar Namadi, ya bayyana matukar jin dadinsa bisa wannan gagarumin tallafi, da ya haɗa da bayar da kayayyaki da jari ga rukunin al’umma daban-daban.

Yana mai nuni da cewar, wannan mashahurin shiri ya nuna kyakkyawan hangen nesa na Shugaban karamar hukumar, Alhaji Tasi’u Adamu, wajen tallafa wa mutanen karkara da ke fama da kalubale daban daban.

Namadi, ya kaddamar da rabon tallafi ga mutane fiye da 350 a karamar hukumar Sule Tankarkar.

Wakilinmu ya aiko mana da rahoton cewar, an gudanar da rabon tallafin wanda ya hada da tallafin karatu ga matasa 80 da aka sama musu guraben karatu a manyan jami’o’i da kwalejoji a faɗin kasar nan, da rabon babura ga mutane 30, sai keken ɗinki da aka rabawa mata 30.

Kazalika, an raba kekunan hawa 30 ga ɗalibai, da injin niƙa guda 10 da aka rabawa matsakaitan ‘yan kasuwa.

Sai kuma tallafin jari na naira dubu dari 2 da aka rabawa ‘yan kasuwa har su  20 da tallafin jari na naira dubu 100 ga ƙananan ‘yan kasuwa guda 20.

Sauran su ne tallafin jari na naira dubu hamsin hamsin ga mutane 30, da kuma bayar da naira dubu ashirin ashirin ga mutane 100, domin rage radadin halin da ake ciki, da rabon shagunanan tafi da gidanka guda 3 ga matasa masu kasuwanci.

Har ila yau, an raba babura masu kafa 3, na daukan kaya guda 2 ga matasa, sai kuma bayar da mukullin gidaje masu ɗaki biyu ga matasa guda 4 daga sassa daban-daban na karamar hukumar Sule Tankarkar.

A don haka, Gwamnan ya yi kira ga sauran shugabannin ƙananan hukumomi na jihar da su yi koyi da irin wannan gagarumin aikin  na Tasiu Adamu domin al’umma su ci gaba da sharbar romon mulkin dimokradiyya.

Ya bayyana cewar irin waɗannan ayyuka ne ke taka muhimmiyar rawa wajen rage talauci da samar da ayyukan yi ga jama’a.

Taron ya samu halartar jama’a daga sassa daban-daban na jihar, inda aka bayyana wannan shiri a matsayin abin alfahari ga al’ummar Sule Tankarkar da Jihar Jigawa baki daya.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90 a Borno

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya sanar da rage kashi 90 na tallafin rabon kayan abinci don ƙarfafa dogaro da kai a tsakanin mazauna jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin da yake ƙaddamar da rabon kayan abinci ga magidanta 25,000 gabanin watan Ramadan a Maiduguri, Jere da sauran sassan jihar.

Helikwaftan farko ƙirar Najeriya zai fara aiki —NASENI Sarkin Musulmi ya ba da umarnin dubin watan Ramadan

A cewar Zulum, gwamnatin jihar za ta ba da fifiko ga hanyoyin samar da ci gaba na tsawan lokaci a kan matakan agaji na gajeren lokaci kamar rabon tallafin abinci.

Ya kuma bayyana irin gagarumin jarin da gwamnatinsa ta yi wajen tallafa wa manoma sama da miliyan ɗaya da muhimman kayayyakin amfanin gona kamar irin su iri, taki, famfunan ban-ruwa, maganin ƙwari da magungunan kashe ciyawa.

“Wannan dabarar ba kawai za ta inganta dogaro da kai ba ce har ma da rage kashe kuɗaɗen gwamnati,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, rabon kayan tallafin zai taƙaita ne ga ƙananan hukumomin jihar guda biyu kawai daga cikin 27  a shekarar 2025 saboda ƙalubalen da suke fuskanta.

“Ƙananan Hukumomin da za su sami tallafin abinci a shekara mai zuwa su ne: Ngala da Kala-Balge saboda yanayi na musamman.

“Waɗannan yankuna sun fuskanci mummunar ɓarna a gonakinsu daga giwaye kuma sun fuskanci ambaliyar ruwa. Don haka, a shekarar 2025, gwamnatin Jihar Borno za ta samar da kayayyakin tallafin abinci ga Ngala da Kala-Balge kaɗai,” inji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Masallacin Juma’a A Garin Samamiya Da Ke Birnin Kudu
  • Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano
  • NAHCON Ta Naɗa Sabon Sakatare
  • Kwara ta Raba Littafai Fiye da Dubu 74 Kyauta Ga Dalibai
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Ce Har Yanzu Akwai Guraben Biyan Kujerar Hajji
  • Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90 a Borno
  • Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90% a jihar
  • Gwamna Sule Ya Hori Masu Ziyarar Ibada Ta Kirista Su Zama Jakadu Na Gari
  • Gidauniyar Sarki Salman Ta Rab Tallafin Abinci Ga Mutane 2,450 A Kebbi
  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙaddamar Da Shirin Tallafin Abinci Na Naira Biliyan 4