Karamar Hukumar Sule Tankarkar Ta Raba Kayayyakin Tallafi Ga Al’ummarta
Published: 26th, January 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta yaba da shirin tallafawa al’umma da Shugaban karamar hukumar Sule Tankarkar ya bullo da shi a yankin.
Gwamnan Jihar, Mallam Umar Namadi ya bayyana haka a lokacin da ya halarci taron kaddamar da rabon tallafin da aka gudanar a karamar hukumar.
Malam Umar Namadi, ya bayyana matukar jin dadinsa bisa wannan gagarumin tallafi, da ya haɗa da bayar da kayayyaki da jari ga rukunin al’umma daban-daban.
Yana mai nuni da cewar, wannan mashahurin shiri ya nuna kyakkyawan hangen nesa na Shugaban karamar hukumar, Alhaji Tasi’u Adamu, wajen tallafa wa mutanen karkara da ke fama da kalubale daban daban.
Namadi, ya kaddamar da rabon tallafi ga mutane fiye da 350 a karamar hukumar Sule Tankarkar.
Wakilinmu ya aiko mana da rahoton cewar, an gudanar da rabon tallafin wanda ya hada da tallafin karatu ga matasa 80 da aka sama musu guraben karatu a manyan jami’o’i da kwalejoji a faɗin kasar nan, da rabon babura ga mutane 30, sai keken ɗinki da aka rabawa mata 30.
Kazalika, an raba kekunan hawa 30 ga ɗalibai, da injin niƙa guda 10 da aka rabawa matsakaitan ‘yan kasuwa.
Sai kuma tallafin jari na naira dubu dari 2 da aka rabawa ‘yan kasuwa har su 20 da tallafin jari na naira dubu 100 ga ƙananan ‘yan kasuwa guda 20.
Sauran su ne tallafin jari na naira dubu hamsin hamsin ga mutane 30, da kuma bayar da naira dubu ashirin ashirin ga mutane 100, domin rage radadin halin da ake ciki, da rabon shagunanan tafi da gidanka guda 3 ga matasa masu kasuwanci.
Har ila yau, an raba babura masu kafa 3, na daukan kaya guda 2 ga matasa, sai kuma bayar da mukullin gidaje masu ɗaki biyu ga matasa guda 4 daga sassa daban-daban na karamar hukumar Sule Tankarkar.
A don haka, Gwamnan ya yi kira ga sauran shugabannin ƙananan hukumomi na jihar da su yi koyi da irin wannan gagarumin aikin na Tasiu Adamu domin al’umma su ci gaba da sharbar romon mulkin dimokradiyya.
Ya bayyana cewar irin waɗannan ayyuka ne ke taka muhimmiyar rawa wajen rage talauci da samar da ayyukan yi ga jama’a.
Taron ya samu halartar jama’a daga sassa daban-daban na jihar, inda aka bayyana wannan shiri a matsayin abin alfahari ga al’ummar Sule Tankarkar da Jihar Jigawa baki daya.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
Wannan nasarar ta nona irin namijin kokarinda Bankin ya yi na kara habaka samar wa da kansa kudaden shiga duk da matsin tattalin arzikin da kasar nan ke fuskanta.
Bugu da kari, kadarorin Bankin sun karu zuwa jimmlar kaso 47 daga Naira tiriliyan 20 a shekarar 2023 zuwa Naira tiriliyan 30, a shekarar 2024.
Kazalika, abokan huddar Bankin sun karu zuwa kashi 45, wanda kudaden da suka ajiyarsu ya karu zuwa Naira tiriliyan 22 a shekarar 2024, sabanin yadda ya ke kan Naira tiriliyan 15, a shekarar baya.
Duk da samun hauhawan farashin kaya a kasar, Bankin ya samu karin kudaden shigar Bankin, sun karu zuwa kashi 38.9, sabanin kashi 36.1.
Bankin na da yakinin samun ribar shiyar da ta kai ta Naira 4.00, wadda ta kai jimlar ribar shiyar Naira 5.00 da ya samu a shekara.
Shugaba kuma Manajin Darakta na rukunonin Bankin Dakta Adaora Umeoji, da yake yin bayani kan wannan nasarra da Bankin ya samu ya sanar da cewa, nasarar da Bankin ya samu a shekarar, ta nuna irin jajircewar da Bankin ya ke ci gaba da yi, wajen gudanar da ayyukansa, musamman ta hanyar yin amfani da fasahar zamani.
“Zamu kuma ci gaba da mayar da hankali wajen kara habaka fanninin mu na hada-hadar kudade, kara inganta ayyukan mu da farantawa abokan huddar mu da masu ruwa da tsaki rai,”. Inji Bankin Dakta Adaora.
A cewar Shugaban na rukunonin Bankin na Zenith, za mu kuma ci gaba da kara karfafa wanzar da shugabancin mu a fannin hada-hadar kudade na kasar nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp