Zantawa Da Shugaban Kasar Sri Lanka Anura Kumara Dissanayake
Published: 26th, January 2025 GMT
Wakilin babban rukunin gidajen rediyo da talibijin na kasar Sin (CMG) kwanan nan ya tattauna tare da shugaban kasar Sri Lanka Anura Kumara Dissanayake, wanda ya kawo ziyara kasar Sin a karon farko tun bayan hawansa mulki.
Da yake magana game da nasarar da kasar Sin ta samu na zamanantar da kanta, Dissanayake ya bayyana cewa, yawan al’ummar kasar Sin ya kai kusan kashi daya bisa biyar na al’ummar duniya, amma kasar Sin ba ta da kashi daya bisa biyar na albarkatun duniya.
এছাড়াও পড়ুন:
An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar
An fara gudanar da bukukuwan ranar soji a Iran a ranar 18 ga watan Afrilu ta hanyar gudanar da faretin soja a gaban shugaban kasar Mas’ud Pezeshkian
An fara faretin soji na sojojin kasar Iran a kusa da hubbaren Imam Khumaini (r.a) da ke kudancin birnin Tehran fadar mulkin kasar a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan ranar sojoji ta 18 ga watan Afrilu.
A jiya Juma’a 18 ga watan Afrilu ne sojojin kasar Iran suka fara faretin soji na murnar zagayowar ranarsu da kuma irin bajintar jarumtakar sojojin kasar, a kusa da hubbaren Imam Khumaini (r.a) da ke kudancin babban birnin kasar Tehran.
A cewar kamfanin dillancin labaran IRNA na Iran, faretin ya samu halartar shugaban kasar Mas’ud Pezeshkian da manyan kwamandojin sojojin kasar Iran.
Faretin dai zai kunshi rundunonin yaki da motoci masu sulke na rundunar sojojin kasa na kasar, mayakan sojin sama, makamai da na’urorin tsaro na sojojin sama, da na’urorin sojan ruwa da ake iya jigila da su.
Haka kuma za a baje kolin wasu daga cikin nasarorin da Iran ta samu, da makamai masu linzami, na sama, da na ruwa, da kuma na kasa gami da jiragen sama marasa matuka ciki.