Leadership News Hausa:
2025-03-01@14:20:21 GMT

Zantawa Da Shugaban Kasar Sri Lanka Anura Kumara Dissanayake

Published: 26th, January 2025 GMT

Zantawa Da Shugaban Kasar Sri Lanka Anura Kumara Dissanayake

Wakilin babban rukunin gidajen rediyo da talibijin na kasar Sin (CMG) kwanan nan ya tattauna tare da shugaban kasar Sri Lanka Anura Kumara Dissanayake, wanda ya kawo ziyara kasar Sin a karon farko tun bayan hawansa mulki.

Da yake magana game da nasarar da kasar Sin ta samu na zamanantar da kanta, Dissanayake ya bayyana cewa, yawan al’ummar kasar Sin ya kai kusan kashi daya bisa biyar na al’ummar duniya, amma kasar Sin ba ta da kashi daya bisa biyar na albarkatun duniya.

Ya ce Kasar Sin ta dage kan bin hanyar ci gaba da ta dace da ita, kuma kasar ta samu ci gaba, jama’arta kuma suna rayuwa da aiki cikin kwanciyar hankali. Ya ce, ina ganin yin nazari a kan hanyar ci gaban kasar Sin wani abu ne da ya kamata mu yi, musamman yadda za mu iya koyon abubuwa masu daraja da yawa daga gogewarta. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Da Saudiyya Sun Tattauna Kan Taron OIC Mai Zuwa

Kasashen Iran da kuma Saudiyya sun tattauna kan halin da ake ciki a yankin dama batun taron kungiyar kasashen Musulmi ta OIC da za’ayi a cikin kwanaki masu zuwa a Jeddah.

Tattaunawar ta wakana ne ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Saudiyya Yarima Faisal bin Farhan da Abass Araghchi, ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran (RII).

A yayin ganawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan halin da ake ciki a yankin, tare da tattauna taron ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar OIC da za a yi a Jeddah.

Dama a kwanan baya bangarorin sun tattauna kan shirin shugaban Amurka Donald Trump na kwace zirin Gaza dama tilasta wa falasdinawan yankin kaura zuwa Masar da Jordan, shirin da dukkan kasashen biyu sukayi fatali da shi.

Araghchi ya la’anci shirin na Amurka da ‘yan sahyoniya na tilastawa al’ummar Gaza komawa wasu kasashe a matsayin ci gaba da shirin ‘yan mulkin mallaka na shafe Falasdinu, yana mai jaddada bukatar daukar kwararan matakai na kasashen duniya don tunkarar wannan makirci.

Ya kuma yi kira ga al’ummar musulmi da sauran al’ummar duniya baki daya da su dauki matakin gaggawa kan lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abubuwan Sha Domin Karin Ni’ima Ga Mata
  • An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House
  • Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
  • Shugaban kasar Guinea-Bissau a ya yi wata ganawa da shugaban kasar Rasha
  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Tabbatar Da Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • Iran Da Saudiyya Sun Tattauna Kan Taron OIC Mai Zuwa
  • Sin Za Ta Kara Matsa Kaimi Ga Raya Sha’anin Mata Na Duniya
  • Sheikh Na’im Kasim Ya Gana Da Ministan Harkokin wajen Kasar Iran Da Shugaban Majalisar Dokoki
  • Mugunta Fitsarin Fako…
  • Wakilin Sin: Dole Ne A Aiwatar Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza