Leadership News Hausa:
2025-03-31@18:58:03 GMT

Zantawa Da Shugaban Kasar Sri Lanka Anura Kumara Dissanayake

Published: 26th, January 2025 GMT

Zantawa Da Shugaban Kasar Sri Lanka Anura Kumara Dissanayake

Wakilin babban rukunin gidajen rediyo da talibijin na kasar Sin (CMG) kwanan nan ya tattauna tare da shugaban kasar Sri Lanka Anura Kumara Dissanayake, wanda ya kawo ziyara kasar Sin a karon farko tun bayan hawansa mulki.

Da yake magana game da nasarar da kasar Sin ta samu na zamanantar da kanta, Dissanayake ya bayyana cewa, yawan al’ummar kasar Sin ya kai kusan kashi daya bisa biyar na al’ummar duniya, amma kasar Sin ba ta da kashi daya bisa biyar na albarkatun duniya.

Ya ce Kasar Sin ta dage kan bin hanyar ci gaba da ta dace da ita, kuma kasar ta samu ci gaba, jama’arta kuma suna rayuwa da aiki cikin kwanciyar hankali. Ya ce, ina ganin yin nazari a kan hanyar ci gaban kasar Sin wani abu ne da ya kamata mu yi, musamman yadda za mu iya koyon abubuwa masu daraja da yawa daga gogewarta. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID

Kungiyar bada agajin ta gaggauwa ta “white Helmets” na kungiyar Al’kaida, wacce kuma take samun tallafin gwamnatin Amurka ta hukumar USAID ta rasa tallafin da take don gudanar da ayyukanta.

Kamfanin dillancin labaran Spunik na kasar Rasha ya bayyana cewa, kasashen yamma musamman Amurka sun yi amfani da kungiyar ta Al-qaeda a lokacin yakin kasar Syriya a shekara ta 2011 zuwa 2017 don ingiza kasashen yamma kan gwamnatin kasar Siriya na cewa ta yi amfani da makaman guba a kan mutane, don cimmmai manufofinsu a kasar ta Siriya.

A halin yanzu dai shugaban Trump zai dakatar da tallafin da ya ke bawa kungiyar mai yuwa saboda sun cimma manufarko a kasar Siriya ta kifar da gwamnatin Bashar a Al’asad. A kalla mutane kimani 40 daga cikin kungiyar ne suka tabbatar da cewa a lokacin yakin sun kai hare kan sojojin Bashar Al-asad, sannan sun yi amfani da wani yaro dan sheakara 5 Omran don farfaganda kan gwamnaton Bashar Al-Asad, kamar yadda mahaifinsa ya fallasa daga baya.

Kasashen Amurka Burtania da Nethalanda duk sun taimakawa kungiyar da miliyoyin dalar Amurka don gudanar da ayyukansu. Amma a bana shugaba Trump ya yanked alar Amurka miliyon 30 da aka warewa kungiyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Girgizar Kasa: Shugaban Kasar Myanmar Ya Mika Godiya Ga Tawagar Likitocin Yunnan Ta Kasar Sin
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Yi Wa Musa Dadis  Camara Afuwa
  • Hezbulla: Iran Ce Babbar Mai Goyon Bayan Al-Ummar Falasdinu
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Fiji: Ya Kamata A Koyi Fasahohin Da Kasar Sin Ta Samu A Fannin Raya Kasa
  • Shugaba Xi Ya Jajantawa Shugaban Myanmar Game Da Girgizar Kasar Da Ta Auku
  • Najeriya : An samu hargitsi a yayin jerin gwanon ranar Kudus a Abuja
  • Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya
  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  • Sharhi: Taruka Da Gangamin Ranar Quds Ta Duniya 2025
  • Manyan Amfanin Gona Biyar Da Ya Kyautu Manoma Su Zuba Hannun Jari A 2025