Leadership News Hausa:
2025-04-19@21:22:16 GMT

Kwanaki Bayan Kashe Masunta 20, Boko Haram Ta Kashe Sojoji 20 A Borno

Published: 26th, January 2025 GMT

Kwanaki Bayan Kashe Masunta 20, Boko Haram Ta Kashe Sojoji 20 A Borno

Majiyoyin leken asirin da suka tabbatar da harin, sun kara da cewa maharan sun kai hari sansanin ne dauke da muggan makamai, inda suka ce ‘yan ta’addan sun lalata gine-gine da dama da kuma motocin aikin soji a yayin harin.

.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ya kashe masoyin tsohuwar matarsa bayan sakinta a Neja

Wani mutum mai suna Muhammad Ma’aba daga ƙauyen Fujeregi da ke Ƙaramar hukumar Gbako a Jihar Neja, ya mutu a hannun tsohon mijin matar da yake shirin aura.

Rahotanni sun bayyana cewa, wata Ƙungiya ƙarƙashin jagorancin tsohon mijin matar mai suna Alhaji Yikangi, daga ƙauyen Yikangi Chikan ne suka kai wa Ma’aba hari a tsakanin garin Saganuwa da Fujeregi.

PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – Wike Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia

Mazauna garin sun shaida wa Daily Trust cewa, tsohon mijin ya saki matar mai suna Fatima Suleiman sau uku, amma ya dage cewa ba za ta ƙara aure ba — ko da ta samu sabon mai neman aurenta.

Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce, “A ranar 17/4/2025 da misalin ƙarfe 2:00 na rana, an samu labarin cewa wasu gungun mutane ƙarƙashin jagorancin wani Alhaji Yikangi na ƙauyen Chikan ta hanyar Lemu sun kai hari kan wani Muhammad Ma’aba na ƙauyen Fujeregi, dukkansu a ƙaramar hukumar Gbako.

“An samu rahoton cewa wanda aka kashe ɗin an yi masa dukan tsiya ne saboda rashin fahimtar da wata mata Fatima Suleiman da suke cikin yanki ɗaya, ya mutu a hanyar zuwa babban asibitin Lemu, inda aka tabbatar da mutuwarsa.”

Abiodun ya ƙara da cewa, ana gudanar da bincike kan lamarin, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin kamo waɗanda suka aikata wannan aika-aika.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 8 Kan Zargin Kashe Jariri A Borno
  • Ndume Ya Yaba wa Sojoji Kan Daƙile Harin Boko Haram A Gwoza
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Harin Amurka Na Jiya A Yemen Ya Kai 74
  • Ya kashe masoyin tsohuwar matarsa bayan sakinta a Neja
  • Boko Haram Sun Kashe Sojoji 2 Da Wasu A Wani Sabon Hari A Borno
  • An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno
  • Amurka Ta Kashe Mutane 38 Tare Da Jikkata Fiye Da 100 A Harin Da Ta Kai Lardin Al-Hudaidah Na Yemen
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun
  • Matan da suka tsira daga Boko Haram na buƙatar tallafin musamman
  • An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato