Bugu da kari, a ran 25 ga watan kuma, CMG ya gabatar da wannan bidiyo a kasar Jamus, inda gidajen sinima na manyan biranen kasar ciki har da Berlin da Frankfurt, da Dresden da kuma Dortmund da sauransu, suka watsa wannan bidiyo.

Kazalika, a ran 24 ga watan, a birnin Asuncion, hedkwatar kasar Paraguay, an fara watsa wannan bidiyo a manyan allunan dake titunansa har tsawon kwanaki 7 masu zuwa a jere.

Wannan shi ne karon farko da aka watsa irin wannan bidiyo a wannan kasa dake kudancin nahiyar Amurka.

An ba da labari cewa, UNESCO ta shigo da bikin bazara bisa kalandar gargajiya ta kasar Sin, wato Bikin Bazara cikin jeren sunayen dake wakiltar kayayyakin al’adun gargajiya na tarihi da aka gada daga kaka da kakanni a shekarar 2024, matakin da ya bayyana cewa, al’adun bikin na kara yaduwa zuwa duk fadin duniya zuwa wani sabon matsayi.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta

Ƙungiyar Hamas ta ce tana goyon bayan komawa yarjejeniyar tsagaita wuta a Zirin Gaza, tana mai cewa za ta yi amfani da shawarar da masu shiga tsakanin suka bayar wadda za ta kai ga sakin ƙarin fursunonin Isra’ila biyar da kuma tsagaita wuta a Gaza tsawon kwana 50.

Babban jami’in Hamas da baya zaune a Gaza, Khalil al-Hayyam, ya ce ƙungiyar ta amince da ƙudirin da masu shiga tsakani daga Masar da kuma Qatar suka gabatar.

Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone Ladubban Ranar Idin Karamar Sallah

Ofishin firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ma ya ce ya karɓi tayin, amma ya gabatar da nasa tayin ”wanda ya ci karo da wanda masu shiga tsakanin suka gabatar masa, a ƙarƙashin jagorancin Amurka.”

BBC ya ruwaito cewa idan har ya tabbata, sabon shirin tsagaita wutar ya zo daidai da bakin ƙaramar Sallah da musulmai suka fara a ranar Lahadi.

A ranar Asabar, ofishin Nethanyahu ya ce ya yi zaman tuntuɓa game da sabon tayin da masu shiga tsakani suka gabatar masa.

Ya kuma ce ya gabatar da nasa sharaɗin, wanda Amurka ta yi amanna da shi, duk da cewa ofishin bai yi ƙarin bayani a kai ba. Itama Amurka ba ta kai ga cewa komai ba a kai kawo yanzu.

Wannan na zuwa ne yayin da dakarun Isra’ila suka ƙaddamar da sabbin hare-hare a Rafah da sassan Gaza bayan ƙarewar wa’adin tsagaita wutar da aka ƙulla a ranar 19 ga watan Janairu tsakanin ɓangarorin.

Tun bayan ƙarewar wa’adin har yanzu ɓangarorin sun gaza amincewa da fara aiwatar da zango na biyu na yarjejeniyar tsagaita wutar.

A zangon farko na yarjejeniyar tsagaita wutar dai Hamas ta saki ƴan Isra’ila 33, kuma har yanzu tana ci gaba da riƙon wasu 59, duk da dai ana zaton wasu daga cikin su sun mutu.

A baya dai Hamas ta haƙiƙance kan aiwatar da yarjejeniyar a yadda take tun farko, da kuma tattauna zango na biyu wanda zai kai ta ga sakin sauran mutanen da ta yi garkuwa da su, da kuma kawo ƙarshen yaƙin baki ɗaya ta hanyar janyewar dakarun Isra’ila daga Gaza.

Sai dai Isra’ila da Amurka sun nemi a tsawaita wa’adin zangon farko na yarjejeniyar wanda ya ƙare a watan da ya gabata, ba tare da fayyace yadda za a kawo ƙarshen yaƙin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana Share Fagen Gudanar Bikin Baje Kolin Kayayyakin Da Ake Shigar Da Su Kasar Sin Yadda Ya Kamata
  • Faransa : An haramta wa Marie Le Pen, takara har tsawon shekaru 5
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
  • Gwamna Umar Namadi Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Sallah Karama
  • Girgizar Kasa: Shugaban Kasar Myanmar Ya Mika Godiya Ga Tawagar Likitocin Yunnan Ta Kasar Sin
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta
  • Siriya : Ofishin jakadancin Amurka ya yi gargadi game da yiyuwar hare-hare a yayin bikin sallah
  • Adadin mamata a girgizar kasar Myanmar ya ka 1,644
  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya