Shugaban kasar Sin Xi Jinping da sauran jagorori na kasar Sin sun ziyarci ko kuma sun gayyaci wasu su ziyarci tsoffin jami’ai da suka yi ritaya, sun mika gaisuwa gabanin bikin Bazara na al’ummar Sinawa na ranar 29 ga watan Janairun nan.

Xi, wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban kwamitin koli na sojan kasar, da sauran jagororin kasar, sun taya tsoffin jami’an da suka yi ritaya murnar bikin Bazara, tare da musu fatan karin lafiya da kuma tsawon rai.

A nasu bangaren kuwa, tsoffin jami’an da suka yi ritaya sun yaba da ayyukan kwamitin koli na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin a shekarar da ta gabata, tare da bayyana goyon bayansu ga muhimmin matsayin shugaba Xi a kwamitin kolin JKS da ma jam’iyyar baki daya.

Kazalika, sun bayyana fatan ‘yan jam’iyyar da sojoji da jama’ar dukkan kabilu za su kara hada kai da kara kusantar kwamitin koli na jam’iyyar tare da kwamared Xi Jinping a matsayin jigon gina kasar Sin zuwa kasa mai matukar karfi da kuma cimma nasarar farfado da al’ummar Sinawa ta hanyar zamanatarwa irin ta Sin. (Mohammed Yahaya)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno 

Wata gobara ta ƙone gidajen wuccin gadi sama da 100 ma ’yan gudun hijira a  sansanin ’yan gudun hijira na hukumar ruwa da ke Ƙaramar Hukumar Monguno ta Jihar Borno.

Shaidu sun ce ba a samu asarar rai ba a gobarar da ta tashi da misalin karfe 10.40 na safe na ranar Alhamis da ta gabata, kuma cikin sauri ta bazu a unguwar, inda ta ƙona kayan abinci, da sauran kadarori masu ɗimbin yawa.

Majiyar da ke sansanin ta bayyana cewar an tura jami’an agaji zuwa wurin domin kula da jama’a da kuma hana sace-sacen kayayyakin jama’a da suka rage, yayin da jami’an kashe gobara tare da mazauna sansanin suka yi bakin ƙoƙarinsu wajen kashe wutar.

Tashin gobarar dai ba shi ne karo na farko ba a wannan sansanin, domin ko da a kwanakin baya ma an samu makamancin hakan, lamarin ya sa jama’a ke zargin akwai sakaci daga wasu mazauna wannan sansanin.

Kada Kanawa su bari rigingimun siyasa su hana su zaman lafiya — Shettima Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem

Don haka suka jadadda buƙatar a riƙa yin hattara don kauce wa ci gaba da faruwar irin haka nan gaba, kasancewar yanayin bazara mai dauke da iska ne ke ƙara ƙaratowa a wannan yanki, wanda hakan kan haifar da barazanar yawaitar tashin gobara a lokacin bazara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji
  • Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno 
  • Ma’aikatar Lafiya Ta Yemen Ta Sanar Da Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Hare-Haren Amurka Kan Kasar
  • Putin ya umarci tsagaita wuta a Ukraine albarkacin bikin Ista
  • An buɗe wa jami’an NDLEA wuta a Abuja
  • ‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara
  • Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.
  • 2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Harin Amurka Na Jiya A Yemen Ya Kai 74
  • Kwamitin Gudanar da Kasuwa Maras Shinge Ta Maigatari Sun Ziyarci Fadar Gumel