Aminiya:
2025-04-18@14:26:17 GMT

An saki Falasɗinawa 200 da ke ɗaure a Isra’ila

Published: 26th, January 2025 GMT

Isra’ila ta sako Falasɗinawa 200 daga cikin waɗanda take riƙe da su a kurkuku kamar yadda yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninta da ƙungiyar Hamas ta tanada.

Wannan dai na zuwa ne bayan da Hamas ta saki rukuni na biyu na ’yan Isra’ilar da ta yi garkuwa da su — wasu sojojin Isra’ila mata da Hamas take riƙe da su tsawon watanni.

Tinubu zai tafi taron makamashi a Tanzania An ayyana Lakurawa a matsayin ƙungiyar ’yan ta’adda

A wata sanarwa da hukumomin gidan yari na Isra’ila suka fitar sun ce: “Bayan kammala dukkanin abubuwan da suka wajaba a gidajen yarin da kuma amincewar hukumomi an saki dukkanin ’yan ta’addan daga gidajen yari na Ofer da Ktziot,” kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai na AFP da na Reuters suka ce.

Sai dai sabanin Falasɗinawan da aka saki a makon da ya gabata waɗanda yawanci hukuncinsu na zaman gidan yari kaɗan ne, a wannan karon, 121 daga cikin fursunonin suna kan hukuncin rai da rai ne — wasu bisa laifin kisan kai fiye da sau daya da ya hada da kisan farar hula ’yan Isra’ila.

Shekarun Falasɗinawa fursunonin sun bambanta sosai, inda mafi ƙanƙanta da aka saki shi ne mai shekara 16, yayin da mai shekara 69 ya kasance mafi girma a cikinsu.

Ɗaya daga cikin fursunonin ya shafe shekara 39 a gidan kurkukun Isra’ila, bayan da aka kama shi da farko a 1986.

Waɗanda aka yanke wa hukuncin manyan laifuka mafiya tsanani ba sa cikin waɗanda aka saki yau.

Kusan 70 daga cikinsu za a fitar da su daga Isra’ila ne inda za a bi da su ta Masar zuwa ƙasashe makwabta da suka haɗa da Qatar da Turkiyya, kafin a kai su Falasɗinu.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Yara Kimani 3,500 Ne Suka Rasa Rayukansu A Taken Medeteranin A Shekaru 10 Da Suka Gabata

Hukumar UNICEF ta MDD mai kula da yara ta bada sanarwan cewa kimani yara 3,500 suka rasa rayukansu a kokarin ketara tekun Medeteranina a cikin shekaru 10 da suka gabata.

Kamfanin dillancin labaran Spunic na kasar Rasha ya nakalto hukumar tana fadar haka a wani rahoton da ta fitar dangane da hakan.

Labarin ya kara da cewa, wannan ya nuna cewa akalla yaro guda ne ya ransa ransa a ko wace rana. Kuma kashi 7/10 daga cikinsu sun halaka ko sun bace ne su kai ba ba tare da rakiyar iyayensu ba. Har’ila yau rahoton ya kara da cewa akalla mutane 20,803 suka halaka a tsakiyar tekun na Mediterranean a kokarinsu na tsallakawa zuwa kasashen na turai.

Daga karshe hukumar tace ba za’a iya sanin hakikanin adadin wadanda suka halaka ba saboda a cikin wasu kwale-kwalen babu wanda ya rayuwa da za’a sami labara daga wajensa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno
  • Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Ta Sake Aiwatar Da Kisan Kiyashi A Sansanin Falasdinawa Na Jabaliya
  • BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano
  • Hamas ta gabatar da shawara kan yarjejeniyar musayar fursunoni da tsagaita wuta
  • Matan da suka tsira daga Boko Haram na buƙatar tallafin musamman
  • Sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kona Yara Da Mata A Harin Da Suka Kai Khum Yunis Na Gaza
  • Yara Kimani 3,500 Ne Suka Rasa Rayukansu A Taken Medeteranin A Shekaru 10 Da Suka Gabata
  • Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza
  • Lauyoyin London Suna Tattara Bayanai Kan ‘Yan Birtaniya Da Suka Yi  Yaki Cikin Sahun Yahudawan Sahayoniyya A Gaza
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Shirin Sakin Dukkanin Fursunonin Isra’ila Bisa Sharuddan Da Ta Gindaya