Aminiya:
2025-04-25@06:09:57 GMT

Gobarar tankar mai ta yi ajalin mutum 18 a Enugu

Published: 26th, January 2025 GMT

An tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 18 sakamakon hatsarin wata tankar mai da ta yi bindiga a Jihar Enugu.

Alƙaluman da mahukunta suka fitar ya nuna cewa hatsarin ya rutsa da mutum 31 ciki har da mutum 10 da suka samu raunuka daban-daban yayin da aka ceto wasu uku da suka tsallake rijiya da baya sai kuma mutum 18 ɗin da suka ƙone ƙurmus.

An yi taron Maulidin ƙasa duk da gargaɗin harin ’yan ta’adda a Kano An saki Falasɗinawa 200 da ke ɗaure a Isra’ila

Hakan na ƙunshe cikin sanarwa da mai magana da yawun rundunar hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa reshen Jihar Enugu, Olusegun Ogungbemide ya fitar da yammacin ranar Asabar.

Sanarwar ta bayyana cewa hatsarin wanda ya auku a sanadiyyar shanyewar birki ya shafi ababen hawa 17 da suka haɗa da tanka ɗaya, motoci 15 da kuma wani babu mai ƙafa uku.

Bayanai sun ce an shiga ruɗanin lokacin da tankar fetur ɗin ta yi bindiga, yayin da take saukowa daga wata hanya mai gangara a wani babban titi mai cunkoso a jihar ta Enugu.

TRT ta ruwaito cewa Kwamandan Hukumar Kare Haɗura ta Ƙasa a jihar, Franklin Agbakoba Onyekwere ya ce ya je wajen amma bai yi ƙarin bayani ba.

Tankar man ta kama da wuta ne ƙasa da mako guda bayan mutane fiye da 100 sun mutu yayin da wata tankar mai ta yi bindiga a Jihar Neja.

Kamfani Dillancin Labarai na Anadolu ya ba da rahoton cewa, Nijeriya ta fuskanci hatsarin tankar mai 172 inda mutane 1,896 suka mutu tun daga 2009, a yayin da matsalar ta fi muni a 2024, inda jimillar mutanen da suka mutu suka kai 266.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce a yanzu jihar na ɗaya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Najeriya.

Ya ce, a matsayinsa na babban jami’in shari’a da tsaro a Jihar Yobe, yana da haƙƙin ganin an bi doka don tabbatar da cewa jihar ta samu zaman lafiya.

An kama mata 2 na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin karɓar lambar karramawa da aka yi masa shi da wasu shugabnnin da Ƙungiyar Inganta zaman lafiya ta “Peace Building Development Consult” (PBDC) ta yi musu.

Gwamnan wanda ya samu wakilcin babban lauya kuma Kwamishinan Shari’a na Jihar Yobe, Barista Saleh Samanja, ya bayyana hakan ne ga manema labarai ranar Laraba a Abuja, bayan da ya karɓi lambar yabon ta zaman lafiya.

“ina tabbatar muku kai tsaye cewar, Jihar Yobe tana ɗaya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Najeriya, hakan yana yiwuwa ne saboda haɗin kan da muke bai wa jami’an tsaro da kuma namijin ƙoƙarin da Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ke yi na bada gudummawa kan harkokin tsaro da duk abin da hukumomin tsaro ke son gwamnati ta yi.

“A matsayinsa na babban jami’in shari’a da tsaro na jihar, yana jin cewa yana da haƙƙin ɗabi’a da na shari’a don ba da haɗin kai ga hukumomin tsaro domin mu samu cikakken zaman lafiya a Jihar Yobe,” in ji shi.

A cewarsa wannan karramawar na ƙara ƙarfafa gwiwa ne, inda ya ce Gwamnan zai ci gaba da yin abin da yake yi domin ganin an dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi
  • Sin Da Kenya Sun Daukaka Dangantakarsu Yayin Da Xi Da Ruto Suka Gana
  • Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni
  • Tallafa Wa Al’umma: Ya Dace Gwamnoni Su Yi Koyi Da Jihar Zamfara – UNDP
  • 2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba
  • Ƙasurgumin Ɗan Fashin Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Mutu Bayan Arangama Da ‘Yansanda A Kano
  • Gwamna Inuwa Ya Bayar Da Gudunmawar Naira Miliyan 10 Ga Iyalan Wadanda Hatsarin Ista Ya Rutsa Da Su A Gombe
  •  WHO: Masu Ciwon Koda 400 A Gaza Sun Mutu Saboda Rashin Magani
  • Yawan Falasdinawan Da Suka Yi Shahada Sakamakon Hare-Haren ‘Yan Sahayoniyya Sun Kai 51,266
  • An sanya dokar hana fita ta sa’o’i 12 a Neja