Karya ta kai kwikwiyonta mara lafiya asibiti
Published: 26th, January 2025 GMT
A kwanakin nan ne wani asibitin kula da dabbobi a kasar Turkiyya ya wallafa wani labari mai ratsa jiki na wata karya da ba ta da masauki ta ɗauki ɗanta da ya suma a bakinta ta ajiye shi a kofar asibitin kamar mai neman taimako.
Idan ba don gajeran bidiyon da kyamarorin na’urar CCTV suka ɗauka ba, da alama yawancin mutane za su yi tunanin wannan labarin ba zai iya zama gaskiya ba.
Wani asibitin dabbobi a Unguwar Adnan Kahveci da ke Beylikduzu, a lardin Istanbul na ƙasar Turkiyya, kwanan ya fitar da rahoton ɗaya daga cikin muhimman harkokin asibitin.
A ranar 13 ga watan Janairu, wani masoyin dabbobi ya kawo wani matashin kwikwiyo da suka same shi a kan titi, yana mai cewa shi kaɗai ne ya tsira daga cikin sauran ’yan uwansa.
Jami’an asibitin sun ruga don yi wa ɗan kwikwiyon magani sai ga wata karya ta fito daga bakin ƙofa da wani kwikwiyo a sume a bakinta.
Wani masani ne ya lura da wannan dabbar da ta ƙaurace masa, sai ya garzaya domin ya kula da ’ya’yanta, waɗanda ke fama da rashin lafiya kuma jikinta ya yi rauni sosai.
Kyamarorin sa-ido daga cikin asibitin sun nuna mahaifiyar kwikwiyon da ke cikin damuwa tana bin likitocin dabbobi zuwa asibitin kuma ta zuba musu ido, yayin da suke kula da jaririnta da ya suna.
An yi sa’a, Dakta Baturalp Oghan da tawagarsa sun sami damar ceton ɗan kwikwiyon kuma yanzu dukan karnukan suna murmurewa a asibitin.
“Komai na tafiya yadda ya kamata. Maganin da ake yi wa kwikwiyon da dan’uwansa zai ci gaba na ɗan lokaci kaɗan.
“A wannan lokacin, ba ma karɓar bakin marasa lafiya saboda kula da lafiyarsu,” in ji Dokta Oghan.
“Mahaifiyar karyar tana samun sauƙi sosai. Labarinta ya birge mutane da yawa, karyar tana da basira da kulawa.
“Tana nuna irin soyayyar da uwa karya take yi wa ’ya’yanta.”
A bayyane yake, nonon mahaifiyar ba ya isa ta ci gaba da shayar da sauran ’ya’yanta gaba ɗaya, wanda shi ne dalilin da ya sa wasu ’yan kwikwiyon suka mutu cikin rashin shayarwar, don haka asibitin yana kara kula da ’yan kwikwiyon da suka tsira da ransu da taimakon ciyar da su.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Eidl Fitr: Gwamna Dauda Lawal Ya Buƙaci A Samu Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
Ya ce: “Ya ‘yan uwa Musulmi na Jihar Zamfara da ma sauran wurare, ina miƙa saƙon barka da Sallah tare da taya mu murnar kammala azumin shekarar Hijira ta 1446, wannan wata mai alfarma ta kasance lokaci na sadaukarwa ga Allah (SWT).
“Yayin da muke gudanar da bukukuwan Ƙaramar Sallah, ina kira ga kowannenmu da ya ci gaba da ayyukan ƙwarai, da haƙuri, da karamcin da aka yi a watan Ramadan.
“Ƙalubalan da ke gabanmu suna da yawa kuma suna buƙatar haɗin kai don ganin an magance su, don haka mu ajiye bambance-bambancen da ke tsakaninmu, mu yi aiki tare a matsayin al’umma ɗaya, mu goyi bayan ajandar gwamnati na ceto da sake gina jiharmu.
Gwamna Lawal ya kuma yaba da ƙoƙarin shugabannin addini da na al’umma bisa yadda suke ci gaba da jajircewa wajen samar da zaman lafiya da inganta ɗabi’un da haɗin kan mutane wuri guda.
“Yayin da muke taruwa da masoyanmu domin gudanar da bukukuwan murnar wannan rana, mu sanya jiharmu cikin addu’o’in neman taimakon Ubangiji yayin da muke aiki ba dare ba rana don magance ɗimbin ƙalubalen da ke addabar jihar, Allah SWT ya karbi ibadun mu, ya gafarta mana kurakuran mu, ya kuma albarkaci jiharmu da kasa baki ɗaya tare da samun dawwamammen zaman lafiya da wadatar tattalin arziki. BARKA DA SALLAH”.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp