Aminiya:
2025-03-02@21:53:32 GMT

Ƙungiyoyin da za su fafata da juna a Copa del Rey

Published: 26th, January 2025 GMT

Real Madrid za ta fafata da Leganes, yayin da Barcelona za ta je Valencia a zagayen kwata fainal a Copa del Rey, bayan da aka raba jadawali ranar Litinin.

Wani wasan da zai yi zafi shi ne tsakanin Atletico Madrid da Getafe, yayin da za a yi tata-ɓurza tsakanin Real Sociedad da Osasuna.

Shin wannan ce kaka mafi muni ga Man-United a Gasar Firimiya? Gobarar tankar mai ta yi ajalin mutum 18 a Enugu

Ana sa ran buga wasannin da za a gudanar ranar 5 ga watan Fabrairu.

A jadawalin ya bayar da damar sake buga El Clasico wato karawar hamayya tsakanin Real da Barcelona a wasan ƙarshe da suka daɗe ba su haɗu a gasar tsawon shekaru.

An haɗu a wasan karshe a Copa del Rey karawar El Clasico sau 18, Real ce ta yi nasara 11 daga ciki, wasan baya bayan nan da suka kara shi ne a 2014. Kuma Real Madrid ce ta lashe kofin da cin 2-1 a wasan da aka yi a Valencia.

Sai dai a kakar bana, Barcelona ta caskara Real Madrid karo biyu a baya, wadda ta fara cin 4-0 a Santiago Bernabeu cikin watan Oktoban 2024.

Sai kuma Barcelona ta lashe Spanish Super Cup na bana a kan Real Madrid da cin 5-2 a Saudi Arabia a makon jiya.

Real Madrid ce kan gaba a teburin La Liga da maki 46, sai Atletico Madrid ta biyu da kuma Barcelona ta uku da tazarar maki makwai tsakani da Real.

Barcelona za ta je gidan Valencia a Copa del Rey zagayen kwata fainal, kamar yadda aka raba jaddawali ranar Litinin.

Barcelona ta kawo wannan matakin, sakamakon nasara a kan Real Betis 5-1 ranar Laraba 15 ga watan Janairu a zagayen ‘yan 16.

Ita kuwa Valencia zuwa ta yi ta doke Ourense 2-0 ranar Talata 14 ga watan Janairu.

Valencia da Barcelona za su fuskanci juna a zagayen ’yan takwas ranar Laraba 5 ga watan Fabrairu a filin wasa da ake kira Mestalla.

Jadawalin kwata fainal a Copa del Rey:

Leganes da Real Madrid

Atlético Madrid da Getafe

Real Sociedad da Osasuna

Valencia da Barcelona

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Habasha Da Somaliya Sun Cimma Yarjeniyoyin Fahimtar Juna A Tsakaninsu

A wani mataki na nuna kara kusanci tsakanin kasashen Somaliya da Habasha, shugaban kasar Habasha Abiy Ahmed ya ziyarci Somaliya.

A Shekara guda da ta wuce, kasashen biyu sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna.

Bayan shafe shekara guda ana zaman dar-dar, a watan Disambar da ya gabata ne a kasar Turkiya, kasashen biyu suka sake kulla huldar jakadanci ta hanyar sanya hannu kan yarjejeniyar Ankara.

Shugaban kasar Somaliya Hassan Cheikh Mohamoud ya gabatar a matsayin “mahimmin mataki” na daidaita huldar dake tsakanin kasashen biyu.

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da aka fitar da yammacin jiya Alhamis, an bayyana cewa: Habasha da Somaliya kasashe ne masu dogaro da juna da makoma guda da kuma ra’ayi daya na tabbatar da zaman lafiya da wadata a yankin.

An tattauna dangantakar diflomasiyya, yaki da kungiyoyin ‘yan ta’adda a yankin, da kuma batutuwan tattalin arziki, musamman sha’awar Habasha na samun damar shiga teku.

A halin da ake ciki dai mahukuntan Somaliyan sun dauki matakin saukaka jigilar kayayyaki daga Habasha zuwa tashar jiragen ruwa na Somaliya, musamman na Berbera dake yankin Somaliland.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
  • Babban Sakataren MDD Ya Taya Musulmi Murnar Shiga Watan Ramadan
  • Ban fitar da ran lashe Premier League na bana ba — Arteta
  • Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis
  • Za Mu Doke Atletico Madrid Har Gida, Hansi Flick
  • Gobe Asabar 1 Ga Watan Ramadan 1446
  • Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha
  • An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya 
  • Maraba Da Watan Ramadan
  • Habasha Da Somaliya Sun Cimma Yarjeniyoyin Fahimtar Juna A Tsakaninsu