Ƙungiyoyin da za su fafata da juna a Copa del Rey
Published: 26th, January 2025 GMT
Real Madrid za ta fafata da Leganes, yayin da Barcelona za ta je Valencia a zagayen kwata fainal a Copa del Rey, bayan da aka raba jadawali ranar Litinin.
Wani wasan da zai yi zafi shi ne tsakanin Atletico Madrid da Getafe, yayin da za a yi tata-ɓurza tsakanin Real Sociedad da Osasuna.
Shin wannan ce kaka mafi muni ga Man-United a Gasar Firimiya? Gobarar tankar mai ta yi ajalin mutum 18 a EnuguAna sa ran buga wasannin da za a gudanar ranar 5 ga watan Fabrairu.
A jadawalin ya bayar da damar sake buga El Clasico wato karawar hamayya tsakanin Real da Barcelona a wasan ƙarshe da suka daɗe ba su haɗu a gasar tsawon shekaru.
An haɗu a wasan karshe a Copa del Rey karawar El Clasico sau 18, Real ce ta yi nasara 11 daga ciki, wasan baya bayan nan da suka kara shi ne a 2014. Kuma Real Madrid ce ta lashe kofin da cin 2-1 a wasan da aka yi a Valencia.
Sai dai a kakar bana, Barcelona ta caskara Real Madrid karo biyu a baya, wadda ta fara cin 4-0 a Santiago Bernabeu cikin watan Oktoban 2024.
Sai kuma Barcelona ta lashe Spanish Super Cup na bana a kan Real Madrid da cin 5-2 a Saudi Arabia a makon jiya.
Real Madrid ce kan gaba a teburin La Liga da maki 46, sai Atletico Madrid ta biyu da kuma Barcelona ta uku da tazarar maki makwai tsakani da Real.
Barcelona za ta je gidan Valencia a Copa del Rey zagayen kwata fainal, kamar yadda aka raba jaddawali ranar Litinin.
Barcelona ta kawo wannan matakin, sakamakon nasara a kan Real Betis 5-1 ranar Laraba 15 ga watan Janairu a zagayen ‘yan 16.
Ita kuwa Valencia zuwa ta yi ta doke Ourense 2-0 ranar Talata 14 ga watan Janairu.
Valencia da Barcelona za su fuskanci juna a zagayen ’yan takwas ranar Laraba 5 ga watan Fabrairu a filin wasa da ake kira Mestalla.
Jadawalin kwata fainal a Copa del Rey:
Leganes da Real Madrid
Atlético Madrid da Getafe
Real Sociedad da Osasuna
Valencia da Barcelona
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Yau Lahadi Ce Take Salla A Kasashen Larabawa Da Dama
A kasar Jordan gwamnatin kasar ta bada sanarwan cewa a gobe Litinin ce za’a gudanar da bukukuwan sallah karama bayan azumun watan Ramadan na kwanaki 30.
Muftin kasar ta Jordan Ahmed Hasanat a lokacinda yake bada sanarwan a jiya Asabar yace, ranar Litinin 31 ga watan Maris, ita ce ranar Sallah daya ga watan shawwal shekara ta 1446 Kmariya.
Kasashen Saudia, Qatar, UAE, Kuwait, Bahrain, Yemen, da kuma Palestine sun bada sanarwan cewa yau Lahadi ce sallah karama a kasashensu. Sai kuma kasashen Oman, Siriya da sun bayyana cewa gobe litinin ne salla karama.
A tarayyar Najeriya ma, sultan Sa’ad Abubakar na sokoto ya bada sanarwan sallah a yau Lahadi.
Majalisar koli ta al-amuran musulunci a Najeriya, karkashun shugabancin sultan Sa’ad Abubakar III ne ya bada wannan sanarwan a jiya da yamma.