Aminiya:
2025-03-01@12:22:52 GMT

SERAP ta maka Tinubu da NCC a kotu kan kara kudin kiran waya da data

Published: 26th, January 2025 GMT

Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam da Gaskiya a Harkokin Jama’a (SERAP), ta maka Shugaba Bola Tinubu da Hukumar Sadarwa ta Najeriya (NCC), a kotu kan karan kudin kiran waya da data zuwa kashi 50.

NCC ta amince da karin, wanda ya sa kudin kiran waya ya tashi daga Naira takwas zuwa 16.5 a minti daya, yayin da kudin sayen data 1G ya tashi daga Naira 287.

8 zuwa Naira 431.25.

Shin wannan ce kaka mafi muni ga Man-United a Gasar Firimiya? Ƙungiyoyin da za su fafata da juna a Copa del Rey

 Shi kuwa kudin aika sakon kar ta kwana ya tashi zuwa Naira shida daga na hudu da ake biya a baya.

SERAP, ta ce wannan karin an yi sa ba bisa ka’ida ba, kuma ya saba wa doka tare da keta hakkin ’yan Najeriya na ’yancin yin magana da samun bayanai.

A cikin karar da ta shigar a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, SERAP ta nemi kotu ta dakatar da aiwatar da karin kudin, inda ta ce bai halatta ba.

Kungiyar ta yi zargin cewa NCC ba ta bi ka’ida ba kuma ba ta yi la’akari da tasirin da karin zai yi a rayuwar ’yan Najeriya, wadanda da dama ke fama da tsadar rayuwa.

SERAP, ta jaddada muhimmancin samun sadarwa cikin yanayin mai sauki, inda ta ce hakan wajibi ne don bai wa mutane damar amfani da hakkinsu na ’yancin magana da samun bayanai.

Ta ce karin zai kara tsunduma mutane cikin talauci da kuma kawo nakaso ga harkar sadarwa a fadin Najeriya.

Kungiyar na rokon kotu ta bayar da umarnin dakatar da NCC, wakilanta ko kamfanonin sadarwa daga aiwatar da karin kudin.

Lauyan SERAP, Ebun-Olu Adegboruwa (SAN), ya ce wajibi ne a tabbatar da adalci, bin doka da kuma yin la’akari da yanayin da mutane ke ciki, kafin yanke duk wani hukunci da zai shafi rayuwar jama’a.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar Jiki

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Al’ummar Musulmi na yin azumi ne bisa dalilan addini kamar yadda Allah Ya yi umarni don samun lada.

Sai dai daga baya binciken masana kimiyya ya gano cewa bayan lada da ake samu daga yin azumi, akwai wasu alfanu da mai azumi ke samu ga lafiyar jikin shi da suka haɗa da inganta ƙarfi da zurfin tunani zuwa fitar da gurbatattun abubuwa da jiki ba ya bukata.

A taƙaice dai, ba kawai lada mai azumi ke samu ba, har da samun lafiyar jiki da na ƙwaƙwalwarsa.

NAJERIYA A YAU: Halin da jama’a za su shiga idan Kamfanin Kaduna Electric ya ƙi sauraren ma’aikatansa DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan alaƙar da ke tsakanin yin azumi da kuma lafiyar jikin mutum.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy
  • Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗin 2025 na N54.99trn
  • Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗi na N54.99trn
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar Jiki
  • Gwamnatin Kano ta nemi Tinubu ya kori Aminu Bayero daga fadar Nassarawa
  • Zargin Almundahana: Kotu ta ba da belin Farfesa Usman
  • Iran Za Ta Rubanya Samar Da Wutar Lantarki Ta Makamashin Nukiliya Har Sau Uku Zuwa 2029
  • Gwamna Namadi Ya Nada Jami’an Alhazai 27 Tare Da Kara Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajji
  • Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N825 a Legas
  • Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N860 a Legas