’Yan bindiga sun sace matashiya bayan karɓar kuɗin fansa a Kano
Published: 26th, January 2025 GMT
’Yan bindiga sun kai hari garin Garo da ke Ƙaramar Hukumar Kabo a Jihar Kano cikin daren ranar Lahadi, inda suka sace wata budurwa mai suna Zainab Auwalu, bayan sun karɓi kuɗin fansa Naira miliyan takwas daga hannun mahaifinta.
Zainab, wadda ta kammala makarantar sakandare kwanan nan, an sace ta a gidan mahaifinta, Alhaji Auwalu.
Shaidu sun bayyana cewa ’yan bindigar, kimanin su 10, sun shiga garin da babura ɗauke da muggan makamai.
Sun shiga gidan Alhaji Auwalu da misalin ƙarfe 1:30 na dare, inda suka shafe awanni suna cin karensu ba babbaka, sannan suka tafi da kuɗin fansa tare da sacw ‘yarss.
Wani mazaunin garin, Haruna Muhammad, ya ce harin ya jefa al’ummar garin cikin firgici.
Mutane da yawa na zargin cewa wasu mazauna garin ne suka bai wa ’yan bindigar bayanai.
Kakakin ’yan sandan jihar, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa jami’an tsaro na ƙoƙarin bin sahun ’yan bindigar da kuma ceto matashiyar.
Ko da yake satar mutane da fashi ba su yawaita a Jihar Kano ba, garuruwa irin su Garo da sauran yankunan Arewacin Kano da ke kusa da jihohin Kaduna da Katsina, sun sha fuskantar hare-haren ’yan bindiga.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kada Ku Bari Siyasa Ta Raba Ku – Shettima Ga ’Yan Siyasar Kano
An kuma buƙaci a ci gaba da siyasa cikin fahimta da girmama juna domin amfanin Jihar Kano.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp