Aminiya:
2025-03-02@20:13:37 GMT

Kotu ta ɗaure matashi shekara 2 kan satar wayoyi a Kano

Published: 26th, January 2025 GMT

Wata Kotun Shari’ar Musulunci da ke Fagge ’Yan Alluna a Jihar Kano, ta yanke wa wani matashi hukuncin ɗaurin shekara biyu, a gidan yari bayan samun sa da laifin satar wayoyin salula.

An gurfanar da Aliyu Rabi’u Rijiyar Lemo a gaban kotun, bayan kama shi a kan titin Ibrahim Taiwo tare da wasu biyu, inda suke amfani da Adaidaita Sahu wajen satar wayoyin hannun fasinjoji.

’Yan bindiga sun sace matashiya bayan karɓar kuɗin fansa a Kano ’Yan bindiga sun sace mutum 22 a ƙauyukan Kaduna

A wajen da aka kama shi, wasu fusatattun mtsne sun ƙone Adaidata Sahun da suke amfani da shi wajen aikata laifin.

An tuhume shi da haɗa baki don aikata laifi, sata, da tayar da hankalin jama’a.

Matashin ya amsa laifukan nan gaba ɗaya.

Alƙalin kotun, Khadi Umar Lawan Abubakar, ya yanke masa hukuncin watanni shida a gidan yari ko kuma ya biya tarar Naira 20,000 kan laifin haɗa baki.

Ɗaurin shekara ɗaya a gidan yari kan satar waya, da kuma wata shekara ɗaya kan tayar wa jama’a hankali, ba tare da zaɓin biyan tara ba.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Masar ta ki amincewa da duk wani yunkuri na kafa gwamnatin ‘yan adawa a Sudan

Masar ta jaddada matsayinta kan duk wani yunkuri na kawo barazana ga hadin kan Sudan da ‘yancin kanta da kuma yankinta, tare da yin gargadin cewa kafa gwamnatin rikon kwarya na iya kawo rudani a kasar.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya Lahadi, Ma’aikatar harkokin wajen Masar ta sanar da cewa “Jamhuriyar Larabawa ta Masar ta yi watsi da duk wani mataki da ke kawo barazana ga hadin kan Sudan, ciki har da yunkurin kafa gwamnatin ‘yan adawa, saboda hakan zai kara dagula al’amuran siyasa da kuma kawo cikas ga kokarin hada kan kasar.

Alkahira ta bukaci dukkan bangarorin da su yi aiki mai inganci tare da cikakken tsari na siyasa, da nufin cimma daidaito da kuma maido da tsaro a fadin kasar.

Ta kara da cewa, “Masar ta bukaci dukkan sojojin Sudan da su ba da fifiko ga cin moriyar kasa mafi girma da kuma taka rawar gani wajen bullo da wani cikakken tsari da zai kawo hadin da daidaito ba tare da nuna banbanci ko tsoma bakin kasashen waje ba.”

Ministan harkokin wajen Sudan Ali Youssef al-Sharif ya tabbatar a karshen watan da ya gabata cewa “babu wanda zai amince da abin da ake kira gwamnatin hadaka a Sudan, kuma babu wata kasa da za ta amince da ita.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masar ta ki amincewa da duk wani yunkuri na kafa gwamnatin ‘yan adawa a Sudan
  • Zargin Neman Yin Lalata: Ina Da Kwararan Hujjoji Akan Akpabio – Natasha 
  • Shugabar Tanzaniya Ta Yaba Da Yadda Ake Ci Gaba Da Samun Karuwar Jigilar Kayayyaki A Tashar Tanga Da Sin Ta Inganta
  • Zelensky : Ban Ga Laifin Da Na Yi Wa Trump, Ballantana In Nemi Afuwa
  • Sarkin Sasa ya rasu bayan shafe shekaru 125 a doron ƙasa
  • Yadda ake ‘Spring rolls’
  • MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy
  • Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas
  • Gwamnatin Kano Ta Shirya Taron Bita Don Jami’an Watsa Labarai
  • Buhari ya koma Kaduna da zama bayan shafe shekara 2 a Daura