Kotu ta ɗaure matashi shekara 2 kan satar wayoyi a Kano
Published: 26th, January 2025 GMT
Wata Kotun Shari’ar Musulunci da ke Fagge ’Yan Alluna a Jihar Kano, ta yanke wa wani matashi hukuncin ɗaurin shekara biyu, a gidan yari bayan samun sa da laifin satar wayoyin salula.
An gurfanar da Aliyu Rabi’u Rijiyar Lemo a gaban kotun, bayan kama shi a kan titin Ibrahim Taiwo tare da wasu biyu, inda suke amfani da Adaidaita Sahu wajen satar wayoyin hannun fasinjoji.
A wajen da aka kama shi, wasu fusatattun mtsne sun ƙone Adaidata Sahun da suke amfani da shi wajen aikata laifin.
An tuhume shi da haɗa baki don aikata laifi, sata, da tayar da hankalin jama’a.
Matashin ya amsa laifukan nan gaba ɗaya.
Alƙalin kotun, Khadi Umar Lawan Abubakar, ya yanke masa hukuncin watanni shida a gidan yari ko kuma ya biya tarar Naira 20,000 kan laifin haɗa baki.
Ɗaurin shekara ɗaya a gidan yari kan satar waya, da kuma wata shekara ɗaya kan tayar wa jama’a hankali, ba tare da zaɓin biyan tara ba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Baffa Bichi, Kabiru Rurum, Sha’aban Sharada Da Wasu Sun Koma Jam’iyyar APC
Tsoffin kwamishinoni na Jihar Kano kamar su Hon. Diggol, Hon. Abbas Sani da Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Baffa Bichi su ma sun koma APC.
Hakazalika, Hon. Sha’aban Ibrahim Sharada wanda ya tsaya takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar ADP a zaɓen 2023, ya sauya sheƙa zuwa APC.
Ana kallon wannan sauya sheƙar a matsayin wani babban tagomashi ga jam’iyyar APC musamman a Jihar Kano.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp