An gurfanar da masoyan da suka kai wa malami hari a Kano
Published: 26th, January 2025 GMT
Wata ɗaliba daga Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, mai suna Khadija Hassan Chiranchi, da kuma saurayinta Khalid Hussain wanda aka fi sani da Baffa, sun gurfana a gaban kotun Shari’ar Musulunci kan zargin kai wa malami hari.
Rahotanni sun bayyana cewa, Khadija ta gayyato saurayinta Khalid zuwa ofishin malamin, Aliyu Hamza Abdullahi, wanda ta ce yana zame mata matsala a karatunta.
A lokacin ne saurayin ya zaro adda ya sari malamin a kai.
Dukkaninsu sun gurfana a kotu kan tuhume-tuhumen da suka haɗa da, haɗa baki, aikata daba, kutse da cin zarafi.
Sun musanta zargin da ake musu, inda suka ce kotun ba ta da hurumin sauraron shari’ar.
Duk da haka, alƙalin kotun ya bayar da umarnin a tsare su a gidan yari har zuwa ranar 27 ga Fabrairu, 2025, don sake gurfanar da su.
Sai dai kuma, an zargi saurayin da mallakar makami mai hatsari, wanda ya amince da laifin.
Wanda a nan ne kotun ta ce tana da hurumin sauraron wannan ɓangaren na zargin, wanda ya sa aka ɗage shari’ar zuwa wannan rana domin ci gaba da sauraron ta.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
LEADERSHIP HAUSA Ta Bayyana Wadanda Suka Yi Nasara A Gasar Gajerun Labaran Soyayya
Wadanda Suka Yi Nasara
Aliyu Usman Adam – Matsayi na daya
Aliyu Usman Adam, dan asalin Zariya ta Jihar Kaduna, an haife shi a shekarar 1984. Ya kammala karatunsa na firamare da sakandare a Zariya, sannan ya samu digiri a harshen Hausa daga Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya a 2008. Bayan hidimar kasa a Jihar Edo, ya yi aiki a kamfanin SAN Yoghurt da kuma Alhuda Center School daga 2011 zuwa 2014.
A 2014, Aliyu ya koma aikin jarida, inda ya yi aiki da jaridar RARIYA a Abuja har zuwa 2017. A halin yanzu, shi ne Manajan shirye-shirye (Content Manager) a Nishadi TB Abuja. Yana da mata da ‘ya’ya biyu.
Zainab Muhammad (Indian Girl) – Matsayi Na Biyu
Zainab Muhammad, wacce aka fi sani da “Indian Girl,” ‘yar asalin karamar hukumar Dala ce a Kano. Ta kammala firamare da sakandare a Kano, tare da burin ci gaba da karatun jami’a a nan gaba.
Zainab tana da kwazo a bangaren ilimin addinin Musulunci, kuma tana amfani da kafafen sada zumunta wajen ilmantarwa da fadakarwa. A halin yanzu tana da tarin masoya saboda rubuce-rubucenta masu kayatarwa da gina al’umma.
Mujaheed Nuhu Yusuf (Mujaheed Matashi) – Matsayi Na Uku
Mujaheed Nuhu Yusuf, wanda aka fi sani da Mujaheed Matashin marubuci ne a fagen wasan kwaikwayo kuma mawaki daga Kano. Ya wallafa littattafai biyu na wakoki, ciki har da Philosophy Mysterious Pen, wanda ya wallafa tare da marubuci Haiman Ra’ees.
Mujaheed shi ne shugaban kungiyar marubuta Ruhin Adabi, kuma yana wallafa rubuce-rubucensa a shirin Bakandamiya Hikaya da kuma shafinsa na Facebook.
Wannan gasa ta kara tabbatar da aniyar LEADERSHIP HAUSA na bunkasa hadaka da kirkirar rubutu a cikin al’ummar Hausawa. Jaridar na shirin ci gaba da shirya irin wadannan gasar domin karfafa sha’awar adabi da kuma karfafa dangantaka da masu karatu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp