An Gudanar Da Taron Tattauna Batun Murkushe Magoya Bayan Falasdinawa A Kasar Burtaniya
Published: 26th, January 2025 GMT
Bayan da jami’an tsaro a kasar Burtania suka kama wani fitaccen mai gwagwarmayar kare hakkin Falasdinawa da kuma goya masu baya, a kwanakin da suka gabata. Wasu yan kasar sun gudanar da taro don tattaun makomar incin fadin albarkacin baki a kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wadanda suka yi magana a taron a yau Lahadi, suna cewa batun encin fadin albarkacin baki, da kuma kare hakkin b il’adama yana kara tabarbarewa a kasar.
Labarin ya kara da cewa a ranar asabar da ta gabata ce, masu zanga-zanga a manya manyan birana a kasar Burtaniya suna fito kan tituna inda suke, goyon bayan al-ummar Falasdinu, sun bukaci a kawo karshen mamayar kasar Falasdinu, a kawo karshen goyon bayan da kasashen yamma suke bawo HKI kan Falasdinawa. A kawo karshen mamayar kasashen larabawa sannan a sake gida zirin gaza bayan rusashi wanda HKI a cikin watanni 15 da suka gabata.
A birnin londan kadai, yawan masu zanga-zanga ta lumana sun kai kimani 80,000, sun bukaci a kawo karshen takurawar da suke wa kasashen Lebanon da Iran.
A yayin zanga-zangar dai yansanda sun kama mutane kimani 77 suka kuma gurfanar da su a gaban Kotu. Sanan sun bukaci fitattun yan siyasar kasar wadanda suke cikin zanga zangar wato Jeremy Corbyn tsohon shugaban jam’iyyar Labo da kuma dan majalisa John McDonnell duk su kai kansu gaban jami’an tsaro don amsa tambayoyi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu
Kasashen Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu domin cin moriyar juna a matsayinsu na makobta.
Wannan bayyanin ya fito bayan tattaunawa data wakana tsakanin ministocin harkokin wajen kasashen biyu a birnin Yamai bayan kwashe watanni ana takaddama.
Yayin ziyarar da ministan harkokin wajen Najeriya ya kai Nijar an gudanar da wani babban taro tsakanin shugabannin diflomasiyyar kasashen biyu don sake farfado da hanyoyin hadin gwiwa a bangarori da dama da suka hada da tattalin arziki da tsaro.
Ministan harkokin waje da hadin gwiwa na Nijar Bakary Yaou Sangaré da takwaransa na Najeriya Yusuf Maitama Tuggar sun gana a ranar 16 ga ga watan nan, lamarin dake nuni da wani gagarumin sauyi na dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu da ta yi tsami tsawon watanni biyo bayan juyin mulkin da ya faru a ranar 26 ga watan Yulin 2023.
bangarorin biyu sun kuma tattauna kan barazanar ta’addanci a kan iyakokinsu, inda suka jaddada aniyarsu ta hada karfi da karfe wajen yakar kungiyoyin da ke dauke da makamai da ke kawo cikas wajen aiwatar da dukkanin shirye-shiryen ci gaba a kasashen biyu cikin shekaru da dama. Inda suka bukaci ma’aikatun tsaron kasashen biyu da su ci gaba da hadin gwiwa a fannin tsaro.
Dangantaka tsakanin kasashen biyu da ke makwabtaka da juna ta tabarbare ne a lokacin da Najeriya ta taka muhimmiyar rawa wajen daukar matakan kakabawa Yamai takunkumin da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ta ECOWAS ta kakabawa kasar, wanda hakan ya bata dangantakar da ke tsakaninsu.