An Gudanar Da Taron Tattauna Batun Murkushe Magoya Bayan Falasdinawa A Kasar Burtaniya
Published: 26th, January 2025 GMT
Bayan da jami’an tsaro a kasar Burtania suka kama wani fitaccen mai gwagwarmayar kare hakkin Falasdinawa da kuma goya masu baya, a kwanakin da suka gabata. Wasu yan kasar sun gudanar da taro don tattaun makomar incin fadin albarkacin baki a kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wadanda suka yi magana a taron a yau Lahadi, suna cewa batun encin fadin albarkacin baki, da kuma kare hakkin b il’adama yana kara tabarbarewa a kasar.
Labarin ya kara da cewa a ranar asabar da ta gabata ce, masu zanga-zanga a manya manyan birana a kasar Burtaniya suna fito kan tituna inda suke, goyon bayan al-ummar Falasdinu, sun bukaci a kawo karshen mamayar kasar Falasdinu, a kawo karshen goyon bayan da kasashen yamma suke bawo HKI kan Falasdinawa. A kawo karshen mamayar kasashen larabawa sannan a sake gida zirin gaza bayan rusashi wanda HKI a cikin watanni 15 da suka gabata.
A birnin londan kadai, yawan masu zanga-zanga ta lumana sun kai kimani 80,000, sun bukaci a kawo karshen takurawar da suke wa kasashen Lebanon da Iran.
A yayin zanga-zangar dai yansanda sun kama mutane kimani 77 suka kuma gurfanar da su a gaban Kotu. Sanan sun bukaci fitattun yan siyasar kasar wadanda suke cikin zanga zangar wato Jeremy Corbyn tsohon shugaban jam’iyyar Labo da kuma dan majalisa John McDonnell duk su kai kansu gaban jami’an tsaro don amsa tambayoyi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Yi Allawadai Da Sabon Harin HKI A Kasar Lebanon
Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bakin kakakinta Dr. Isma’ila Baka’i, ta yi tir da sabbin hare-haren da HKI ta kai wa kasar Lebanon a daidai lokacin da ake bikin ranar Kudus.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na kasar ta Iran ya bayyana cewa; Abinda HKI ta yi keta tsagaita wutar yaki ne,wanda abin a yi tir da shi ne.
Haka nan kuma ya yi ishara da nauyin da ya rataya akan wuyan Majalisar Dinkin Duniya da kuma sauran kasashen da suke cikin sa-ido da ‘yarjeneniyar tsagaita wutar yaki, haka nan kuma ya yi kira zuwa ga kungiyoyin kasa da kasa da su dauki mataki na gaggawa domin kawo karshen maimaita keta tsagaita wutar yaki da ‘yan sahayoniyar suke yi.
Har ila yau, kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya ce; “ Dalilin da ‘yan sahayoniya su ka bijiro da shi na kai wa Lebanon hari,ba zai zama karbabbe ba, don haka wajibi ne ga kungiyoyin kasa da kasa da su dauki matakin yadda ‘yan sahayoniyar suke keta wutar yaki a cikin Gaza, Lebanon da kuma Syria.
Dr. Baka’i ya bayyana abinda HKI take yi da cewa, baraza ce ga zaman lafiya da sulhu na duniya.
Tun bayan tsagaiwa wutar yaki a kasar Lebanon, HKI tana keta ta a duk lokacin da ta so, kamar kuma yadda ta kafa sansanoni biyar da ta girke sojojinta a ciki.