MDD Ta Bayyana Cewa Halin Da Ake Ciki A Kudancin Kasar Lebanon Ba Ta Komawar Mutane Ba
Published: 26th, January 2025 GMT
Wasu jami’an MDD sunn bayyana cewa, a cikin halin da ake ciki a kudancin kasar Lebanon ba ya yuwa mutane yankin su koma gidajensu.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ba bayyana cewa a yau ne wa’adin kwanaki 60 na ficewar sojojin HKI daga kudancin kasar Lebanon kamar yadda ya zo a cikin yarjeniyar da suka cimma da gwamnatin kasar Lebanon watanni biyu da suka gabata.
A safiyar yau ne sojojin HKI suka kashe mutan akalla 15 sannan wasu kimani 83 suka ji rauni a lokacinda suka yi kokarinn komawa gidajensu da ke kudancin kasar Lebanon wadanda sojojin HKI suke mamaye su.
Wakilin MDD na musamman a kan al-amuran kasar Lebanon Jeanine Hennis-Plasschaertand da kuma shugaban rundunar UNIFEL ta MDD Lt. Gen. Aroldo Lázaro
Sun bayyana cewa a cikin halin da ake ciki a kudancin kasar Lebanon. Sun fada a wani taro da kakafafen yada labarai kan cewa lokaci bai yi ba don komawa garuruwan da suke kudancin kasar Lebanon.
Jami’an na MDD sun bayyana cewa, lokacin da aka ayyana a yarjeniyar tsagaita budewa juna wuta na ficewar hki daga yankin bai yi ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jigawa Za Noma Rabin Shinkafa Da Ake Amfani Da Ita A Nigeria Nan Da 2030
Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya ce gwamnatinsa na shirin bayar da gudunmawar kashi 50 na shinkafar da Najeriya ke bukata nan da shekara ta 2030.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar tawagar hukumar tattara kudaden shiga da kasafi (RMAFC) karkashin jagorancin shugaban kwamitin inganta kasafin kudi da kasafin kudi, Ambasada Desmond Akawor, yayin ziyarar ban girma da suka kai a gidan gwamnati dake Dutse.
Ya bayyana cewa, suna noman shinkafa sau biyu a shekara, inda ya nuna cewa, a shekarar 2024 kadai, sun noma sama da hekta 200,000 na shinkafa.
Ya yi nuni da cewa, a bana, suna son noma sama da hekta 250,000 wanda a shekarar 2030, burinsu ya kai kadada 500,000.
Malam Umar Namadi ya ce, a irin takun da suke tafiya za su cimma hakan cikin sauki.
“Babban burinmu shi ne mu ba da gudummawar metric ton miliyan 3.6 na shinkafa kowace shekara don noman shinkafar Najeriya – wanda ke wakiltar kusan kashi 50% na abin da al’ummar kasar ke bukata. Muna da kasa, jama’a, da siyasa don ganin hakan ta tabbata.”
Gwamna Namadi ya ce har yanzu noma shi ne jigon tattalin arzikin Jigawa, inda kusan kashi 85% na al’ummarta ke tsunduma a wannan fanni, inda ya ce gwamnatinsa ta samu nasarorin tarihi a harkar noman rani a yankunan da ba su da yawa a jihar.
Dangane da tallafin albarkatun kasa, gwamnan ya bayyana irin ma’adinan da ba a yi amfani da su a Jigawa ba, ciki har da mai, amma ya bayyana yadda gwamnati ke taka-tsantsan wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro.
Tun da farko, shugaban tawagar RMAFC ya shaida wa gwamnan cewa ziyarar na daga cikin ayyukan da kwamitin ya ba su na tantance ayyukan da suka dace a matakin jihohi ta hanyar ware kudaden shiga na musamman na kasa da kashi 1.68 cikin 100 da nufin karkatar da tattalin arzikin Najeriya, tare da mai da hankali kan noma, yawon bude ido, da ma’adanai masu inganci.
Ya ci gaba da cewa kwamitin ya yaba da yadda aka fara gabatar da jawabai da ziyarce-ziyarcen wuraren da aka fara yi, musamman irin abubuwan da suka shafi albarkatun kasa a jihar, kuma za su ci gaba da duba harkokin noma tare da baiwa gwamnan tabbacin tantance gaskiya.
Ya kuma jaddada muhimmancin amfani da albarkatun kasa domin bunkasar tattalin arziki.
KARSHE/USMAN MZ