MDD Ta Bayyana Cewa Halin Da Ake Ciki A Kudancin Kasar Lebanon Ba Ta Komawar Mutane Ba
Published: 26th, January 2025 GMT
Wasu jami’an MDD sunn bayyana cewa, a cikin halin da ake ciki a kudancin kasar Lebanon ba ya yuwa mutane yankin su koma gidajensu.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ba bayyana cewa a yau ne wa’adin kwanaki 60 na ficewar sojojin HKI daga kudancin kasar Lebanon kamar yadda ya zo a cikin yarjeniyar da suka cimma da gwamnatin kasar Lebanon watanni biyu da suka gabata.
A safiyar yau ne sojojin HKI suka kashe mutan akalla 15 sannan wasu kimani 83 suka ji rauni a lokacinda suka yi kokarinn komawa gidajensu da ke kudancin kasar Lebanon wadanda sojojin HKI suke mamaye su.
Wakilin MDD na musamman a kan al-amuran kasar Lebanon Jeanine Hennis-Plasschaertand da kuma shugaban rundunar UNIFEL ta MDD Lt. Gen. Aroldo Lázaro
Sun bayyana cewa a cikin halin da ake ciki a kudancin kasar Lebanon. Sun fada a wani taro da kakafafen yada labarai kan cewa lokaci bai yi ba don komawa garuruwan da suke kudancin kasar Lebanon.
Jami’an na MDD sun bayyana cewa, lokacin da aka ayyana a yarjeniyar tsagaita budewa juna wuta na ficewar hki daga yankin bai yi ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
A gaban mijina Akpabio ya fara neman kwanciya da ni —Sanata Natasha
Sanata Natasha Akpoti ta zargi Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswil Akpabio da neman yin lalata da ita.
’Yar Majalisar Dattawa daga Jihar Kogi ta bayyana cewa mijinta ma shaida ne a kan yunkurin Akpabio ne yin lalata da ita.
A wata hira da aka yi da ita a tashar talabijin ta Arise a safiyar Juma’a, Sanata Natasha ta ce tun da ta ki amincewa da buƙatar Shugaban Majalisar ya kafa mata ƙahon zuƙa.
A makon da ya gabata ne Natasha ta yinwa Akpabio wankin babban bargo a zauren Majalisar bayan ya sauya mata kujera ba tare da tuntubar ta ba.
Shin Kwankwasiyya ta kama hanyar wargajewa ne? NAJERIYA A YAU: Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar JikiYa ba da umarnin ne bayan da ’yan majalisar suka kada ƙuri’ar amincewa da hakan, domin tabbatar da dokokin zauren Majalisar.
Daga bisani ya tura lamarin ga kwamitin ladabtarwar majalisar ta gudanar da bincike tare da gabatar da rahoto cikin makonni biyu.
Ana cikin haka ne ’yar majalisar ta maka shi a kotu tana neman diyyar Naira biliyan 100.03.
A wata hira da aka yi da ita a tashar talabijin ta Arise a safiyar Juma’a, Sanata ta ce, tana da hujjoji da hotunan saƙonnin da ya aika mata.
’Yar Majalisar ta ce Akpabio ya sha kiran ta ta manhajar WhatsApp, sa’annan ta buƙaci Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta bibiyi wayar da suka yi domin gano gaskiya.
Ta bayyana cewa ta sha neman gabatar da kudiri kan Masana’antar Mulmula Karfe na Ajaokuta a zauren Majalisar amma Akpabio yana kin sanya batun a jerin abubuwan da za a tattauna a majalisar.
Ta ce daga bisani bayan ta nuna damuwarta wasu sanatoci suka bukaci ta je ta yi masa magana saboda muhimmancin masana’antar.
Ta ce, da ta yi masa magana sai ya ce, “Sanata Natsaha, a matsayina ba shugaban majalisar nan, Ni ke da wuƙa da nama. Ya kamata ki ba ni kulawa, domin idan kika kuka da ni za ki samu alherai masu yawa.”
Ta ce, ko da ta bayyana masa cewa ba ta fahimta ba sai ya ce, “ya rage naki.”
Ta ce, “wannan abun da ke faruwa da ni daidai yake da na malamin da ke wahalar da ɗalibarsa saboda ta ƙi kwanciya da shi.”
Ta bayyana cewa tun a shekarar 2023 Akpabio ya fara yi mata wannan mummunan tayi a lokacin da ita da mijinta suka ziyarce shi domin taya shi murnar zagayowar ranar haihuwarsa.
Ta ce “yana rike da hannuna muna zagayawa yana nuna mana cikin gidansa, mijina na biye da mu, sai ce zai soma ce na zo gidansa mu huta.
“Mijina da ke biye da mu ya ji maganar, saboda haka ya hana mu tafiya ƙasar waje ni kadai ko in yi tafiya da Akpabio shi kadai.”