Sojojiun HKI A Kudancin Kasar Lebanon Sun Kashe Mutane Fararen Hula Wasu Kuma Suka Ji Rauni A Yau Lahadi
Published: 26th, January 2025 GMT
Ministan kiwon lafiya na kasar Lebanon ya bada sanarwan cewa sojojin HKI a kudancin kasar sun kashe fararen hula 15 sannan wasu 83 suka ji rauni a safiyar yau.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana cewa mutanen kudancin kasar Lebanon sun komawa gidajensu da suke kudancin kasar kan iyaka da kasar Falasdinu da aka mamaye ne, sai sojojin yahudawan, suka bude masu wuta suka kashe wannan adadin.
A yau Lahadi ne 26 ga watan Jeneru ne, wa’adin ficewar sojojin HKI daga kasar Lebanon yake cika kamar yadda ya zo cikin yarjeniyar da suka sanyawa hannu da kasar Lebanon watanni biyu da suka gabata.
Wannan bas hi ne kate hurumin yarjeniyar da aka sanyawa hannu da HKI ba, tun bayana tsagaita wuta sojojin yahudawan suka fara kutsawa cikin wasu yankuna a kasar ta Lebanon. Sun kuma kashe wasu mutanen kasar wadanda suka samu a cikin gidajensu a kan iyakar kasashen biyu, duk da cewa an kulla yarjeniyar zaman lafiya.
Tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta bada labarin cewa a yau Lahadi ma, sojojin yahudawa sun kama mutane biyu yan kasar Lebanon a garin haula na kudancin kasar. Sannan wani jirgin yaki wadanda ake sarrafashi daga nesa ya yi harbi a wasu yankuna na kudancin kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mutum 10 a wani sabon hari a Filato
Aƙalla mutum 10 ne suka rasu, yayin da wasu uku suka jikkata sakamakon harin da wasu mahara suka kai wa al’ummar Ruwi da ke Ƙaramar Hukumar Bokkos, a Jihar Filato.
Maharan sun kai harin ne a daren ranar Alhamis, inda suka buɗe wuta kan mutanen da suka halarci wata jana’iza da misalin ƙarfe 9:30 na dare.
’Yan sanda sun haramta hawan Sallah a Kano An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a ZamfaraWani mazaunin yankin ya ce: “Mummunan hari ne. Sun zo kwatsam suka fara harbi. Muna roƙon hukumomin tsaro da su ɗauki mataki don kare al’ummarmu.”
Rundunar ’yan sandan jihar, ta tabbatar da faruwar harin, amma ba ta bayyana adadin waɗanda suka rasu ba.
Kakakin rundunar, DSP Alabo Alfred, ya ce, “Kwamishinan ‘yan sanda ya tura ƙarin jami’an tsaro da kayan aiki don wanzar da zaman lafiya.
“Za mu tabbatar da cewa waɗanda suka aikata wannan aika-aika sun fuskanci hukunci.”
Gwamnatin Jihar Filato ta yi Allah-wadai da harin.
Kwamishiniyar Yaɗa Labarai ta jihar, Joyce Ramnap, ta tabbatar wa jama’a cewa ana ɗaukar matakan kawo ƙarshen irin waɗannan hare-hare.
“Gwamnati ba za ta lamunci kashe rayukan ‘yan ƙasa ba. An umarci hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki tare da tabbatar da cewa sun fuskanci hukunci.”