Ministan kiwon lafiya na kasar Lebanon ya bada sanarwan cewa sojojin HKI a kudancin kasar sun kashe fararen hula 15 sannan wasu 83 suka ji rauni a safiyar yau.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana cewa mutanen kudancin kasar Lebanon sun komawa gidajensu da suke kudancin kasar kan iyaka da kasar Falasdinu da aka mamaye ne, sai sojojin yahudawan, suka bude masu wuta suka kashe wannan adadin.

A yau Lahadi ne 26 ga watan Jeneru ne, wa’adin ficewar sojojin HKI daga kasar Lebanon yake cika kamar yadda ya zo cikin yarjeniyar da suka sanyawa hannu da kasar Lebanon watanni biyu da suka gabata.

Wannan bas hi ne kate hurumin yarjeniyar da aka sanyawa hannu da HKI ba, tun bayana tsagaita wuta sojojin yahudawan suka fara kutsawa cikin wasu yankuna a kasar ta Lebanon. Sun kuma kashe wasu mutanen kasar wadanda suka samu a cikin gidajensu a kan iyakar kasashen biyu, duk da cewa an kulla yarjeniyar zaman lafiya.

Tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta bada labarin cewa a yau Lahadi ma, sojojin yahudawa sun kama mutane biyu yan kasar Lebanon a garin haula na kudancin kasar. Sannan wani jirgin yaki wadanda ake sarrafashi daga nesa ya yi harbi a wasu yankuna na kudancin kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram Sun Kashe Sojoji 2 Da Wasu A Wani Sabon Hari A Borno

Ndume, ya yaba wa jarumtakar dakarun Nijeriya, amma ya buƙaci ƙarin matakan tsaro.

Ya buƙaci gwamnati ta taimaka wa ƙungiyoyin tsaron al’umma da kayan aiki da makamai na zamani.

Wannan harin na daga cikin jerin hare-haren da ake fama da su a Jihar Borno a cikin ‘yan kwanakin nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Lebanon Sun Kama Wasu Mutanen Da Suke Shirin Cilla Makamai Kan HKI
  • Yeman : Sojojin Amurka sun kai wani gagarumin farmaki kan lardunan Sanaa da Hudaidah
  • Ma’aikatar Lafiya Ta Yemen Ta Sanar Da Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Hare-Haren Amurka Kan Kasar
  • Tashin Gobara A Kwale-Kwale Ya Lashe Rayukan Mutane 143 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango
  • An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi
  • Sojojin Sudan Sun Kashe ‘Yan Tawayen Kasar Ciki Har Da Manyan Kwamandojinsu A Birnin El Fasher
  • ‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara
  • Boko Haram Sun Kashe Sojoji 2 Da Wasu A Wani Sabon Hari A Borno
  • An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun