HausaTv:
2025-03-01@14:14:01 GMT

Iran Da Afganistan Sun Tattauna Al-Amura Masu Muhiammaci A Kabul

Published: 26th, January 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi  wanda ya jagoranci tawagar yan siyasa da kuma tattalin arzikin kasarsa zuwa birnin Kabul babban birnin kasar Afganistan, a yau Lahadi sun tattauna al-amura masu muhimmanci  tsakaninsu da kuma yanking aba daya.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa ministan ta hadu da tokwaransa na rikon kwarya Amir Khan Muttaki a birnin Kabul inda suka tattauna al-amura da suka shafi kasashen biyu.

Wadanda suka hada da al-amuran kan iyakokin kasashen biyu, tsaro, ruwa da hakkin ko wace kasa kan ruwan da ke kwarara daga kasar Afganistan zuwa kasar Iran. Da batun miliyoyin yan kasar Afgansitan wadanda suke rayuwa a kasar Iran na shekaru kimani 50.

Ministocin biyu sun tattauna al-amura da suka shafi kasashen biyu, wadanda suka hada da makobtaka, musulunci, al-adu da sauransu. Kasashen biyu malobta ne na shekaru aru-aru.

A nashi bangaren Muttaki ya godewa kasar Iran kan daukar bakwantan miliyoyin yan kasar Afganistan, ya kuma bayyana cewa gwamnatin Taliban tana iya kokarinta don ganin sun dawo gida musamman ganin cewa al-amura sun fara kyautata a kasar.

Sannan daga karshe ya ce kasashen biyu zasu yi aiki tare don yaki da yan ta’adda a kasashen biyu musamman a kan iyakokin kasashen biyu

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Habasha Da Somaliya Sun Tattaunawa Hanyoyin Sake Mayar Da Alaka

Fira ministan hakar Habasha  Abiy Ahmed ya sami kyakkyawar tarba daga shugaban kasar Somaliya Hassan Sheikh Mamhud a birnin Mogadishu na Habasa a ranar Alhamis da ya kai ziyara domin bunkasa alaka a tsakainin kasashen biyu.

Sabani a tsakanin kasashen biyu masu makwabtaka da juna ya kunno kai ne a shekarar da ta gabata, bayan da kasar ta Habasha ya kulla yarjejeniya da yankin Somaliland akan tashar jirgin ruwa.

Ita dai kasar ta Habasha ba ta da iyaka da ruwa, don haka take son amfani da mashigar ruwan kasar ta yankin Somaliland. Habashan dai tana son gina wani yanki na kasuwanci a gabar ruwan  ta yankin Somaliland.

 Yankin Somaliland na kasar Somaliya ne wanda Mogadishu  take daukar cewa ba kasa ce mai cin gashin kanta.

Somaliya ta nuna fushinta akan waccan yarjejeniyar tare da zargin Habasha da yin kuste a cikin iyakokin kasarta.

A cikin watan Disamba ne dai Turkiya ta fara shiga tsakanin kasashen biyu domin  warware sabanin da yake a tsakaninsu.

Tattaunawar ranar Alhamis din a tsakanin kasashen biyu ta mayar da hankali ne akan kasuwanci, da tsaro da kuma batun sake mayar da alakar da diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Zama Zakara A Damben Gargajiya Ta 2025 UWW Wanda Aka Gudanar A Kasar Albaniya
  • Iran Da Haddiyar Daular Larabawa Sun Gudanar Da Taron Kwamitin Siyasa Da Al-adu Na Kasashen Biyu
  • Habasha Da Somaliya Sun Tattaunawa Hanyoyin Sake Mayar Da Alaka
  • Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku
  • Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
  • Kasashen Habasha da Nijar sun tattauna kan inganta hadin gwiwar soji da tsaro
  • Habasha Da Somaliya Sun Cimma Yarjeniyoyin Fahimtar Juna A Tsakaninsu
  • Iran Da Saudiyya Sun Tattauna Kan Taron OIC Mai Zuwa
  • Jami’an Diblomasiyyar Kasashen Rasha Da Amurka Zasu Sake Haduwa A Birnin Istambul A Gobe
  • Sheikh Na’im Kasim Ya Gana Da Ministan Harkokin wajen Kasar Iran Da Shugaban Majalisar Dokoki