Iran Da Afganistan Sun Tattauna Al-Amura Masu Muhiammaci A Kabul
Published: 26th, January 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi wanda ya jagoranci tawagar yan siyasa da kuma tattalin arzikin kasarsa zuwa birnin Kabul babban birnin kasar Afganistan, a yau Lahadi sun tattauna al-amura masu muhimmanci tsakaninsu da kuma yanking aba daya.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa ministan ta hadu da tokwaransa na rikon kwarya Amir Khan Muttaki a birnin Kabul inda suka tattauna al-amura da suka shafi kasashen biyu.
Ministocin biyu sun tattauna al-amura da suka shafi kasashen biyu, wadanda suka hada da makobtaka, musulunci, al-adu da sauransu. Kasashen biyu malobta ne na shekaru aru-aru.
A nashi bangaren Muttaki ya godewa kasar Iran kan daukar bakwantan miliyoyin yan kasar Afganistan, ya kuma bayyana cewa gwamnatin Taliban tana iya kokarinta don ganin sun dawo gida musamman ganin cewa al-amura sun fara kyautata a kasar.
Sannan daga karshe ya ce kasashen biyu zasu yi aiki tare don yaki da yan ta’adda a kasashen biyu musamman a kan iyakokin kasashen biyu
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Habasha Da Somaliya Sun Tattaunawa Hanyoyin Sake Mayar Da Alaka
Fira ministan hakar Habasha Abiy Ahmed ya sami kyakkyawar tarba daga shugaban kasar Somaliya Hassan Sheikh Mamhud a birnin Mogadishu na Habasa a ranar Alhamis da ya kai ziyara domin bunkasa alaka a tsakainin kasashen biyu.
Sabani a tsakanin kasashen biyu masu makwabtaka da juna ya kunno kai ne a shekarar da ta gabata, bayan da kasar ta Habasha ya kulla yarjejeniya da yankin Somaliland akan tashar jirgin ruwa.
Ita dai kasar ta Habasha ba ta da iyaka da ruwa, don haka take son amfani da mashigar ruwan kasar ta yankin Somaliland. Habashan dai tana son gina wani yanki na kasuwanci a gabar ruwan ta yankin Somaliland.
Yankin Somaliland na kasar Somaliya ne wanda Mogadishu take daukar cewa ba kasa ce mai cin gashin kanta.
Somaliya ta nuna fushinta akan waccan yarjejeniyar tare da zargin Habasha da yin kuste a cikin iyakokin kasarta.
A cikin watan Disamba ne dai Turkiya ta fara shiga tsakanin kasashen biyu domin warware sabanin da yake a tsakaninsu.
Tattaunawar ranar Alhamis din a tsakanin kasashen biyu ta mayar da hankali ne akan kasuwanci, da tsaro da kuma batun sake mayar da alakar da diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu.