Harkar Murnar Sabuwar Shekara Bisa Kalandar Gargajiyar Sinawa Da Tawagar Sin A MDD Ta Shirya Ta Nuna Al’adun Gargajiya.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama Wanda Ya Kashe Ɗan Bijilanti A Tawagar Sarki Sunusi II

Hukumar Ƴansandan Jihar Kano ta kama wani matashi mai shekaru 20, Usman Sagiru, bisa zargin kashe wani ɗan Bijilanti a tawagar Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II bayan Sallar Eid. Iftila’in ya faru ne da ƙarfe 12:40 na rana a Lahadi, lokacin da ayarin Sarkin Kano ke watsewa daga filin Sallar Idin.

A cewar kakakin Ƴansanda SP Haruna Kiyawa, ana zargi Sagiru da wasu da suka tsere da soka makami ga wani ɗan sa kai mai suna Surajo Rabiu daga unguwar Sabon Titi Jaba, wanda ya mutu sakamakon raunin.

Yadda Sarki Sunusi Lamido Ya Yi Bikin Shiga Fadar Kano Tsakar Dare Khalifan Sheikh Ibrahim Inyas Daga Ƙasar Sanigal Ya Goyi Bayan Sunusi Lamido Sunusi II

Wani ɗan Bijilanti, Aminu Suleman daga Kofar Mata, shi ma ya jikkata a harin wanda yana yanzu yake jinya a Asibitin Murtala Muhammad na Jihar Kano. Waɗannan ‘yan sa kai sun kasance cikin tawagar da ke kare Sarkin Kano a lokacin harin. ‘Yansandan sun bayyana cewa sun fara cikakken bincike kan lamarin, inda suka kuma gayyaci Shamakin Kano, Alhaji Wada Isyaku, domin yi masa tambayoyi dangane da lamarin.

Hukumar ta sake nanata haramcin duk wani irin hawan Sallah a jihar, tare da gargadin cewa za a kai duk wanda aka tarar yana shiga irin waɗannan ayyuka gaban doka. A cewar sanarwar, ‘yan sandan sun dage kan yaƙi da daba da duk wani aiki da zai haifar da tarzoma a jihar, musamman ma a yayin da ake shirye-shiryen bikin Sallah.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muna so a nuna wa duniya mutanen da suka kashe ’yan Arewa a Edo — Gwamnan Kano
  • Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda
  • Gwamna Umar Namadi Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Sallah Karama
  • Ƴansanda Sun Kama Wanda Ya Kashe Ɗan Bijilanti A Tawagar Sarki Sunusi II
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Yi Wa Musa Dadis  Camara Afuwa
  • Tawagar Ma’aikatan Ceto Ta Kasar Sin Ta Isa Birnin Yangon Na Kasar Myanmar 
  • Najeriya : An samu hargitsi a yayin jerin gwanon ranar Kudus a Abuja
  • Rikici Ya Turnuke Jam’iyyar SDP A Yayin Da Aka Samu Shugabanni Bangare Biyu A Kogi
  • Manyan Amfanin Gona Biyar Da Ya Kyautu Manoma Su Zuba Hannun Jari A 2025