Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-03@18:06:33 GMT

An Sami Ambaliyar Ruwa A Gonakin Shinkafa A Jihar Kwara

Published: 26th, January 2025 GMT

An Sami Ambaliyar Ruwa A Gonakin Shinkafa A Jihar Kwara

Gwamnatin Jihar Kwara ta bayyana damuwarta kan ambaliyar rowa a gonakin shinkafa da dama a Shonga, da ke karamar hukumar Edu ta jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamna Rafiu Ajakaye ya fitar,  ya ce  Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya  kafa kwamitin da zai binciki musabbabin ambaliyar.

A cewarsa ana sa ran kwamitin zai ziyarci yankunan da lamarin ya shafa domin gudanar da bincike.

Sanarwar ta ce kwamitin zai kai ziyarar jaje ga Sarkin Shonga Dr. Haliru Yahyah da wadanda abin ya shafa a cikin al’umma.

Mambobin kwamitin da mataimakiyar shugaban ma’aikatan jihar, Gimbiya Bukola Babalola za ta jagoranta, sun hada da kwamishinan ayyukan gona, Mrs Oloruntoyosi Thomas, da kwamishinan muhalli, Hajiya Nafisat Musa Buge; da mai ba da shawara na musamman kan ayyuka na musamman; da  tsaro ga Gwamna,  Alhaji Muhyideen Aliu, da sauransu.

Ali Muhammad Rabi’u

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Kaddamar Da Taro Na 10 Na Zaunannen Kwamitin Majalisar CPPCC Karo Na 14

An kaddamar da taro na 10 na zaunannen kwamitin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin wato CPPCC karo na 14 a yau 1 ga watan Maris a nan birnin Beijing, inda memban hukumar siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta Sin kuma shugaban majalisar CPPCC Wang Huning ya halarci taron.

A gun taron, an zartas da kudurin gudanar da zama na 3 na majalisar CPPCC karo na 14 a ranar 4 ga wannan wata a birnin Beijing, an kuma gabatar da shawara kan ajendar zaman, wato sauraro da yin bincike kan rahoton aiki na zaunannen kwamitin majalisar CPPCC da yadda aka gudanar da ayyukan da aka cimma daidaito a kai, a gun zama na 2 na majalisar CPPCC karo na 14, da halartar zama na 3 na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14, da kuma sauraro da tattaunawa kan aikin gwamnatin kasar da sauran rahotanni. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar Da Shirin Ciyarwar Na Watan Ramadan
  • Yadda ’yan bindiga suka sace ɗalibai 4 a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma
  • Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
  • Mu ne muka kai samame otal ba ’yan bindiga ba — EFCC
  • Kamfanoni 10 Sun Zuba Jarin $466m A Jihar Nasarawa
  • An Kaddamar Da Taro Na 10 Na Zaunannen Kwamitin Majalisar CPPCC Karo Na 14
  • Abubuwan Sha Domin Karin Ni’ima Ga Mata
  • Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250
  • Noman Dabino: Jigawa Ta Yi Hadaka Da Saudiyya