Aminiya:
2025-03-31@15:34:22 GMT

Mace ta rasu, wasu sun jikkata yayin da nakiya ta fashe a Neja

Published: 26th, January 2025 GMT

Wata nakiya ta fashe a Sabon-Pegi da ke Ƙaramar Hukumar Mashegu a Jihar Neja, lamarin ya yi sanadiyyar mutuwar wata mata da kuma jikkata wasu mutum shida.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi, 26 ga watan Janairu, 2025, da misalin ƙarfe 7:30 na safe.

An gurfanar da masoyan da suka kai wa malami hari a Kano Kotu ta ɗaure matashi shekara 2 kan satar wayoyi a Kano

Ya ce lamarin ya faru ne sakamakon wasu nakiyoyi da wani mutum ya ɓoye a wajen domin aikin haƙar ma’adinai.

Lamarin ya yi sanadin lalacewar gidaje kusan 12 a yankin, inda ya jefa al’umma cikin tashin hankali.

Fatima Sadauki ta rasa ranta a wannan mummunan iftila’i, yayin da aka garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Kainji don duba lafiyarsu.

Kwamishinan ’yan sandan Jihar, Shawulu Danmamman, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan lamarin, tare da tura tawagar ƙwararru zuwa wajen domin yin nazari.

Kakakin ya ce mutumin da ya adana nakiyar ya tsere, wanda rundunar ke ci gaba da nemansa.

Rundunar ta tabbatar da daidatar zaman lafiya a yankin, inda ta ce tana ci gaba da sanya ido don hana faruwar irin wannan lamari a gaba.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki

Gwamnatin Jihar Kaduna, ta sanar da shirin ɗaukar ma’aikatan lafiya 1,800 aiki don inganta tsarin Kiwon Lafiya a Matakin Farko (PHC) a faɗin jihar.

Wannan zai taimaka wajen rage matsalar ƙarancin ma’aikata da kuma inganta ayyukan kiwon lafiya a jihar.

Ƙungiyar JNI ta raba wa marayu 50 kayan Sallah a Borno An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara

Kamar yadda Kwamishiniyar Lafiya, Hajiya Umma Ahmad, ta bayyana, wannan mataki zai taimaka wajen rage yawan mace-macen mata masu juna biyu da yara.

“Wannan mataki zai cike giɓin da ake da shi a cibiyoyin lafiya, domin tabbatar da samun ingantaccen kiwon lafiya ga al’ummar Kaduna,” in ji ta.

Gwamnatin jihar ta fara gyara cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 255 tare da samar da kayan aiki na zamani da magunguna.

Wannan zai bayar da damar kula da cututtuka kamar su ciwon suga, hawan jini, da kuma bayar da agajin gaggawa ga mata masu naƙuda.

“Ingantaccen kiwon lafiya ba gata ba ne, haƙƙi ne,” in ji Hajiya Umma, yayin da ta ke jadadda ƙudirin gwamnatin jihar kan kiwon lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  • Talakawa su girmama shugabanni yayin bayyana matsalolinsu — Sarkin Musulmi
  • Kashe Matafiya: Gwamnatin Kano Ta Aika Tawaga Zuwa Edo
  • Rikici Ya Turnuke Jam’iyyar SDP A Yayin Da Aka Samu Shugabanni Bangare Biyu A Kogi
  • Girgizar ƙasa ta hallaka sama da mutum 1000 a Myanmar
  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • Abubuwan Da Za Su Iya Kawo Cikas Ga Bukukuwan karamar Sallah
  • Kisan ’yan Arewa a Edo ya tayar da ƙura