Mace ta rasu, wasu sun jikkata yayin da nakiya ta fashe a Neja
Published: 26th, January 2025 GMT
Wata nakiya ta fashe a Sabon-Pegi da ke Ƙaramar Hukumar Mashegu a Jihar Neja, lamarin ya yi sanadiyyar mutuwar wata mata da kuma jikkata wasu mutum shida.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi, 26 ga watan Janairu, 2025, da misalin ƙarfe 7:30 na safe.
Ya ce lamarin ya faru ne sakamakon wasu nakiyoyi da wani mutum ya ɓoye a wajen domin aikin haƙar ma’adinai.
Lamarin ya yi sanadin lalacewar gidaje kusan 12 a yankin, inda ya jefa al’umma cikin tashin hankali.
Fatima Sadauki ta rasa ranta a wannan mummunan iftila’i, yayin da aka garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Kainji don duba lafiyarsu.
Kwamishinan ’yan sandan Jihar, Shawulu Danmamman, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan lamarin, tare da tura tawagar ƙwararru zuwa wajen domin yin nazari.
Kakakin ya ce mutumin da ya adana nakiyar ya tsere, wanda rundunar ke ci gaba da nemansa.
Rundunar ta tabbatar da daidatar zaman lafiya a yankin, inda ta ce tana ci gaba da sanya ido don hana faruwar irin wannan lamari a gaba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Za Ta Rubanya Samar Da Wutar Lantarki Ta Makamashin Nukiliya Har Sau Uku Zuwa 2029
Jamhuriyar musulunci ta Iran tana shirin aiwatar da shirinta na gina sabbin cibiyoyin samar da wutar lantarki ta hanyar fasahar Nukiliya da kuma fadada wadanda take da su a yanzu.
Shugaban hukumar makamashin Nukiliya ta Iran Muhammad Islami ne ya bayyana hakan, yana mai kara da cewa:
“ Za mu kara yawan wutar lantarkin da muke samarwa da megawati 2000 a kowace sa’a daya daga nan zuwa karshen zangon na bakwai na tsare-tsaren ci gaba da ake yi a kowace shekara 5. Zangon dai zai kare ne a cikn watan Maris 2029.
Salami ya ce za a kara megawati 1,000 a cikin kowace sa’a da hakan zai mayar da abinda ake samarwa zuwa megawati 3,000 a cikin kowace sa’a.