Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF, ya bukaci gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki da su kara himma wajen yara mata na samun damar yin karatu.

Shugaban ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahama Farah, ne ya yi wannan kiran a Kano a wani taron manema labarai na bikin ranar ilimi ta duniya ta 2025.

Ya kara da cewa alkaluma sun nuna cewa ‘yan mata miliyan 7 da 600 ba sa zuwa makaranta, inda shiyyar Arewa maso Yamma da arewa maso gabas ke da kashi 48 cikin 100 na adadin.

Ya danganta wannan kididdigar da abubuwan da suka hada da talauci da ka’idojin zamantakewa da nuna wariyar jinsi, wadanda ke dakile bai wa ‘ya’ya mata damar samun ilimi.

A lokacin da yake gabatar da bitar ayyukan UNICEF na inganta karatun yara mata da kuma ci gaba da karatu, shugaban ofishin kula da kananan yara na jihar Kano, Rahama Mohammed Farah, ya ce asusun ya samu  hadin gwiwa da gwamnati da al’umma wajen magance matsalolin.

Ya ce UNICEF ta kuma yi amfani da tallafin kudi da sauran abubuwan karfafa gwiwa don karfafawa iyaye gwiwa, su yi rajistar ‘ya’yansu mata da tabbatar da ganin sun ci gaba da zuwa makaranta.

Ya yi bayanin cewa, “UNICEF ya yi kokari matuka a wannan fanni, ciki har da bayar da kudade domin karfafa musu gwiwa wajen tura ‘ya’yansu mata zuwa makaranta tare da tallafa musu zuwa matakin sakandare”.

Ya yi bayanin yadda asusun ya ke inganta fasahar rubutu da karatun ‘ya’ya mata ta hanyar cibiyoyin karatun ‘yan mata don ‘yan mata (G4G), inda kimanin ‘yan mata da ke zuwa makaranta miliyan 2 da 600 su ke samun ilimi ta hanyoyin sadarwa da suka hada da rediyo da talabijin a hakin yanzu.

“UNICEF ya kuma inganta kwazon malamai don ilmantar da ‘ya’ya mata, tare da kara yawan malamai a makarantun firamare 42,000“, inji Farah.

Ya yi bayanin cewa UNICEF ya kuma gina tare da gyara wuraren tsaftar ruwa a makarantu 33 a fadin jihohin Kano da Jigawa,  wadanda ‘yan mata 19,622 ke amfani da su.

Ya ce asusun yana kuma  aiki tare da masu tsara manufofi a fannin ilimi don tabbatar da ingantacciyar kariya ga yara da ayyukan makaranta ga yara mata, yayin da kuma yana inganta kwazon malamai  da za su  jagoranci  yara mata.

Taron manema labaran ya samu halartar ‘yan jaridu  daga jihohin Kano,  da Jigawa da Katsina.

Usman Mohammed da Isma’il Adamu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Putin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da Iran

Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta hadin gwiwa daga dukkan fannoni bisa manyan tsare-tsare da Iran a hukumance, a cewar wata takardar aiki da aka wallafa a yanar gizo a jiya Litinin.

Shugaban kasar Rasha da takwaransa na Iran Masoud Pezeshkian sun rattaba hannu kan yarjejeniyar a ranar 17 ga watan Janairu bayan wata tattaunawa da bangarorin biyu suka yi a birnin Moscow.  

Yayin da a ranar 8 ga watan Afrilun nan majalisar dokokin Rasha ta Duma ta amince da yarjejeniyar kana majalisar dattawan tarayyar kasar suka amince da yarjejeniyar a ranar 16 ga Afrilu.

Bisa yarjejeniyar da aka cimma, kasashen biyu na da burin zurfafa da fadada dangantakarsu a dukkan fannonin da suka shafi moriyar juna, da karfafa hadin gwiwa a fannin tsaro, da hada kai wajen gudanar da harkoki a matakin shiyya-shiyya da na duniya baki daya, wanda ya dace da cikakken kawance bisa manyan tsare-tsare kuma na dogon lokaci.

Kazalika, Putin ya jaddada muhimmancin yarjejeniyar, yana mai cewa, ta zayyana “manufar da aka sanya gaba” na zurfafa hadin gwiwa na dogon lokaci.

Kuma an tsara yarjejeniyar ne domin samar da kwanciyar hankali ga dorewar ci gaban kasashen biyu da ma daukacin yankin Eurasia.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za’a Yi Zana’izar Paparoma Francis A Ranar Asabar 26 Ga Watan Afrilu
  • Iyalen Surajo Malumfashi na Radio Nigeria Kaduna Yana Gayyatar Jama’a Zuwa Daurin Auren ‘Yar Sa
  • Putin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da Iran
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Inganta Kiwon Lafiya: Gwamna Buni Ya Ziyarci Sashen Koyar Da Kwararrun Likitoci A Damaturu
  • Hisbah ta kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a Bauchi
  • Inganta Kiwon Lafiya: Gwamna Buni Ya Ziyarci Sabuwar Cibiyar Sayar Da Magunguna Da Ke Damaturu
  • NAJERIYA A YAU: Me ya sa matsalar tsaro “ta gagari gwamnati” a Najeriya?
  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
  • KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030