NAJERIYA A YAU: Dabarun Bunƙasa Kasuwanci Ta Hanyar Intanet
Published: 27th, January 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Ci-gaban zamani ya zo da sauye-sauye da dama a fannonin rayuwa daban-daban ciki har da kasuwanci.
A yanzu hanyar sadarwa ta zamani, ko intanet, tana taka muhimmiyar rawa wajen tallata haja ko saye da sayarwa da ɓangarori da dama.
Tuni ’yan Najeriya da dama suka yi balaguro suka koma intanet da kasuwancinsu.
Shrin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan ƙalubale da ke tattare da wannan harka, da damar da ake samu idan an rungume ta, da kuma dabarun yin nasara a cikinta.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kasuwanci yanar gizo
এছাড়াও পড়ুন:
Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N860 a Legas
Matatar Dangote ta rage farashin man fetur zuwa Naira 825 kan kowace lita a Jihar Legas.
Yanzu haka dai an samu ragin Naira 65, daga farashin da ake siyarwa a baya.
Na gaji bashin 8.9bn a matsayin shugaban APC — Ganduje Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a BornoSabon farashin zai fara aiki daga ranar 27 ga watan Fabrairun 2025.
Matatar ta ce wannan matakin na nufin rage wa ‘yan Najeriya wahalhalun da suke fuskanta, yayin da azumin watan Ramadan ke ƙaratowa, tare da tallafa wa manufofin tattalin arziƙi na Shugaba Bola Tinubu.
“Rage farashin man fetur wani ɓangare ne na ƙokarinmu na sauƙaƙa wa ‘yan Najeriya,” in ji matatar Dangote.
“Za mu ci gaba da tabbatar da wadatar man fetur a farashi mai sauƙi.”
Wannan ragi, na nufin za a sayar da man fetur a gidajen mai a Legas kan Naira 860 kan kowace lita, Naira 870 a Kudu maso Yamma, da Naira 880 a Arewacin Najeriya.
A gidajen mai na AP da Heyden, farashin zai kasance Naira 865 a Legas, sai Naira 875 a Kudu maso Yamma, da Naira 885 a Arewacin Najeriya.
“Muna kira ga ‘yan kasuwa su mara mana baya don tabbatar da cewa ‘yan Najeriya sun ci gajiyar wannan sauƙi,” in ji matatar.