Al’ummar Lebanon Suna Kiran Da Aiwatar Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Kudancin Lebanon
Published: 27th, January 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta bayyana cewa: Tun a shekara ta 2000 al’ummar Lebanon suka tabbatar da cewa su ne jagororin gaskiya a kan tafarkin nasara
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta fitar da wata sanarwa a jiya Lahadi, inda ta jaddada cewa: Daidaiton sojoji da al’umma da kuma ‘yan gwagwarmaya da suke kare kasar Lebanon daga ha’incin makiya ba wai kawai tawada ne a takarda ba, don haka sun daurawa kasashen duniya karkashin jagorancin kasashen da suke daukar nauyin yarjejeniyar da aka cimma alhakin take hakki da laifuffukan makiya yahudawan sahayoniyya tare da tilasta mata ficewa gaba daya daga yankin Lebanon.
Tun daga shekara ta 2000 har zuwa yau, lamarin ya ci gaba da maimaita kansa, domin al’ummar kasar suna tabbatar da cewa: Su ne jagororin gaskiya a kan tafarkin nasara, tare da jarumtakarsu ta sake dawo da fatattakar makiya, tare da tabbatar da cewa babu wani mamaya a cikin wannan kasa mai albarka, wadda aka shayar da kowace hatsi a cikinta da jinin shahidai.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tsawa Ta Kashe Makiyayi Da Shanu A Kudancin Kaduna
Da yake tabbatar da afkuwar lamarin, Malam Tanko Isiyaka, shugaban fulani na gundumar Bondon, ya bayyana cewa marigayin ya fito ne daga jihar Bauchi.
Ya bayyana alhininsa kan faruwar lamarin tare da yin kira da a yi addu’a tare da tallafa wa iyalan mamacin. An yi jana’izar mamacin kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp