HausaTv:
2025-04-02@01:50:14 GMT

Jagoran Kungiyar Ansarullah Ta Yemen Ya Shirin Na Tunkarar Harin Amurka

Published: 27th, January 2025 GMT

Jagoran kungiyar Ansarullah ya bayyana cewa: A shirye suke su tunkari duk wani harin Amurka kuma ya gargadin sojojin haya

Jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyed Abdul-Malik Badruddeen al-Houthi ya tabbatar da cewa: Amurka ta yi amfani da dukkan karfinta wajen tallafawa haramtacciyar kasar Isra’ila da kuma kokarin murkushe al’ummar Falasdinu, yana mai jaddada tsayin daka da matsayarsa da ke tafiya a kan tubalin gaskiya, ikhlasi da ke gudana a tsakanin al’ummar Falastinu da ‘yan gwagwarmayarsu.

Sayyid Abdul-Malik Badruddeen al-Houthi ya bayyana a yayin zagayowar ranar shahadar Sayyid Hussein Badruddeen al-Houthi, cewa: Abin da hukumomi suka yi a shekara ta 2004 kan shahidi wanda shi ne ya kafa tattakin Alkur’ani, kuma shugaba shahidi Hussein Adwan, ba a yi adalci ba, yana mai nuni da cewa abin da shahidin Alkur’ani ya yi shi ne koyar da tarbiyyar Alkur’ani, da kalubalantar masu girman kai da kuma kauracewa kayayyakin Amurka da Haramtaciyyar kasar Isra’il kan matakin da suka dauka na kaddamar da hare-haren wuce gona kan al’ummar kasarsu.

Ya kara da cewa, bayan abubuwan da suka faru a ranar 11 ga watan Satumba, Amurka ta yi shirin mayar da ita tamkar wata kafa ta wani gagarumin yakin neman zabe na tsaurara iko a kan al’ummar kasar, da mamaye yankunanta da kuma kawar da asalinta, ya ci gaba da cewa gwamnatocin da suka mika wuya ga Amurka kuma an bude dukkan kofofin zuwa gare ta, ciki har da gwamnatin Yemen a karkashin taken kawancen yaki da ta’addanci, inda gwamnati a Yemen bayan a abubuwan da suka faru na ranar 11 ga watan Satumba suka bude hanya ga Amurka a cikin soja, tsaro, tattalin arziki, ilimi, kafofin watsa labaru da kuma maganganun addini.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne

Kungiyar Hamasa a gaza ta bada sanarwan cewa ta amince da shawarar da kasashen da suke shiga tskaninta da HKI kan cewa ta amince da kafa gwamnatin hadin kan Falasdinawa, amma ba zata taba mika makamanta ga wani ba ko waye shi.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban Kungiyar Khalil Al-Hayya yana fadar haka a jiya Asabar a wani jawabin da ya gabatar da faifen bidiyo.

Al-Hayya ya kara da cewa muna karban dukkan shawarori masu ma’ana idan an bijirosu gare mua. Amma batun makamanmu, ba zamu taba kyale mutanemmu a hannun yahudawan sahyoniyya ko kuma wasu shuwagabannin Falasdinawa wadanda zasu mika su ga yahudawa ba suna ta yawo da hanka;linsu ba.

Yace fatammu ne gwamnatin HKI ba zata hana zabe gudana a kasar Falasdinu da kuma kafa gwamnatin Falasdinawa a gaza da yankin yamma da kogin Jordan sannan birnin Kudus a matsayin babban birnin kasar ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Ramuwar Gayya Kan Takunkumin Biza Da Amurka Ta Kakaba Wa Jami’anta
  • Ma’aikatan Kasar Sin Sun Ceto Mutum 8 Zuwa Yanzu A Myanmar
  • Ana Zaman Dar-dar A Kasar Zimbabwe Saboda Shirin Zanga-zangar Tsofaffin Sojaji
  • Sojojin Yemen Sun Harbo Jirgin Leken Asirin Amurka Samfurin MQ9
  • Iran ta gargadi Amurka kan barazanar harin bam da Trump ya yi
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen A Daren Jiya
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne