An Bukaci Sarakuna Su Ci Gaba Da Yiwa Al’umma Aiki
Published: 27th, January 2025 GMT
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa, Danladi Jatau, ya bukaci sarakunan gargajiya da su ci gaba da karfafa hadin kai da zaman lafiya a yankunansu domin samun ci gaba a jihar.
Shugaban majalisar ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake jawabi a wajen bikin murnar cika shekaru 5 akan mulki da kuma murnar cika shekaru 50 da haihuwar HRH, Chim Nku, Mista Habila Adamu Aboki a karamar hukumar Akwanga.
Mista Danladi Jatau, wanda ya bayyana muhimmancin hadin kai da zaman lafiya ga ci gaban al’umma, ya kuma yi kira ga sarakunan gargajiya da su ci gaba da sasanta al’ummarsu domin zaman lafiya.
Ya taya sarkin mai daraja ta biyu murnar tare da yi masa fatan Allah ya kara masa lafiya da kariya da kuma hikima a shekaru masu zuwa.
Shugaban majalisar ya kuma bukaci jama’a da su ci gaba da addu’a tare da marawa Gwamna Abdullahi Sule da sauran shugabannin baya domin samun nasara.
Tun da farko, HRH Mista Habila Adamu Aboki, Chim Nku, ya ce ya yanke shawarar shirya taron ne domin ya gode wa Allah a kan rayuwarsa da ta ’yan uwa.
Ya kuma yabawa Gwamna Abdullahi Sule da sarakunan gargajiya da masu ruwa da tsaki da sauran jama’a bisa goyon bayan da suke ba shi don samun nasara.
Basaraken ya yi amfani da wannan damar wajen tabbatar da aniyarsa na inganta hadin kai da zaman lafiya a tsakanin talakawansa.
COV/Aliyu Muraki/Lafia./Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sarakuna Shekara zaman lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya
A Bikin Yawan Sallah na Jafi da aka yi a fadar Sarkin Gombe, Mai Martaba Alhaji Abubakar Shehu Abubakar III, ya yi kira ga manoma da makiyaya da su zauna lafiya da juna.
Sarkin ya ce zaman lafiya shi ne ginshiƙin ci gaba, kuma haɗin kai tsakanin manoma da makiyaya zai hana rikice-rikice da ke barazana ga jihar.
Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano Gwarzon gasar Alƙur’ani ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina“Ina roƙon manoma da makiyaya da su zauna lafiya don guje wa rigingimu.
“Kowa yana da haƙƙin tabbatar da zaman lafiya domin hakan na kawo ci gaban tattalin arziƙi da walwalar al’umma,” in ji Sarkin.
Haka kuma, ya tabbatar da cewa masarautar Gombe za ta ci gaba da goyon bayan gwamnatin jihar domin tabbatar da tsaro mai ɗorewa.
Sarkin ya gode wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa ƙoƙarinsa na inganta rayuwar al’umma da ɗaukar matakan tsaro, musamman samar da motocin aiki ga jami’an tsaro.
Bikin hawan sallah na Jafi ya samu halartar manyan baƙi, ciki har da Gwamnan Jihar Gombe da wasu manyan jami’an gwamnati, inda aka jaddada buƙatar haɗin kai da zaman lafiya a jihar.