An Bukaci Sarakuna Su Ci Gaba Da Yiwa Al’umma Aiki
Published: 27th, January 2025 GMT
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa, Danladi Jatau, ya bukaci sarakunan gargajiya da su ci gaba da karfafa hadin kai da zaman lafiya a yankunansu domin samun ci gaba a jihar.
Shugaban majalisar ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake jawabi a wajen bikin murnar cika shekaru 5 akan mulki da kuma murnar cika shekaru 50 da haihuwar HRH, Chim Nku, Mista Habila Adamu Aboki a karamar hukumar Akwanga.
Mista Danladi Jatau, wanda ya bayyana muhimmancin hadin kai da zaman lafiya ga ci gaban al’umma, ya kuma yi kira ga sarakunan gargajiya da su ci gaba da sasanta al’ummarsu domin zaman lafiya.
Ya taya sarkin mai daraja ta biyu murnar tare da yi masa fatan Allah ya kara masa lafiya da kariya da kuma hikima a shekaru masu zuwa.
Shugaban majalisar ya kuma bukaci jama’a da su ci gaba da addu’a tare da marawa Gwamna Abdullahi Sule da sauran shugabannin baya domin samun nasara.
Tun da farko, HRH Mista Habila Adamu Aboki, Chim Nku, ya ce ya yanke shawarar shirya taron ne domin ya gode wa Allah a kan rayuwarsa da ta ’yan uwa.
Ya kuma yabawa Gwamna Abdullahi Sule da sarakunan gargajiya da masu ruwa da tsaki da sauran jama’a bisa goyon bayan da suke ba shi don samun nasara.
Basaraken ya yi amfani da wannan damar wajen tabbatar da aniyarsa na inganta hadin kai da zaman lafiya a tsakanin talakawansa.
COV/Aliyu Muraki/Lafia./Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sarakuna Shekara zaman lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
An Gayyaci Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Abbas Aragchi Taron Makamashin Nukliya A Amurka
Bayan taro na biyu tsakanin JMI da Amurka a birnin Roma na kasar Italiya a jiya Asabar an gayyaci ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Arachi don gabatar da Jawabi a wani taro wanda mahukuntan kasar Amurka suka shirya.
Kamfanin dillancin labarai IP na kasar ya nakalto masu shirya taron na cewa an gayyace Abbas Arichi don gabatar da jawabin ne don muhuntan Amurka su ji ta bakin wadanda suka kore a sanin amfanin makamashin nukliya ta zaman lafiya da kuma tattaunawa a kansa.
Labarin ya nakalto wadanda suke gudanar da taron wato ” The Carnegie International Nuclear Policy Conference” wanda za’a fara a gobe litinin, na cewa taron yana taimakawa mahukuntan kasar Amurka sanin kan yadda jami’an diblomasiyya yakamata su fahinci abubuwan da suke da sarkakiya a cikin fasahar nukliya.
Har’ila yau ana son jin yadda Iran take gudanar da shirin ta makamacin Nukliya ta zaman lafiya a duk tsawon shekarun da suka gabata.
Labarin ya kara da cewa mai yuwa ministan ya halarci taron ta hotunan bidiyo daga nan Tehran. Labarin ya kammala da cewa taron Amurka da Iran dangane da shirinta na makamashin Nukliya da aka kammala a birnin Ruma ne ya tada wannan bukatar ta jin bangaren Iran dangane da fannonin da ake sarrafa makamashin nukliya ta zaman lafiya.