Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-01@12:32:18 GMT

An Bukaci Sarakuna Su Ci Gaba Da Yiwa Al’umma Aiki

Published: 27th, January 2025 GMT

An Bukaci Sarakuna Su Ci Gaba Da Yiwa Al’umma Aiki

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa, Danladi Jatau, ya bukaci sarakunan gargajiya da su ci gaba da karfafa hadin kai da zaman lafiya a yankunansu domin samun ci gaba a jihar.

 

Shugaban majalisar ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake jawabi a wajen bikin murnar cika shekaru 5 akan mulki da kuma murnar cika shekaru 50 da haihuwar HRH, Chim Nku, Mista Habila Adamu Aboki a karamar hukumar Akwanga.

 

Mista Danladi Jatau, wanda ya bayyana muhimmancin hadin kai da zaman lafiya ga ci gaban al’umma, ya kuma yi kira ga sarakunan gargajiya da su ci gaba da sasanta al’ummarsu domin zaman lafiya.

 

Ya taya sarkin mai daraja ta biyu murnar tare da yi masa fatan Allah ya kara masa lafiya da kariya da kuma hikima a shekaru masu zuwa.

 

Shugaban majalisar ya kuma bukaci jama’a da su ci gaba da addu’a tare da marawa Gwamna Abdullahi Sule da sauran shugabannin baya domin samun nasara.

 

Tun da farko, HRH Mista Habila Adamu Aboki, Chim Nku, ya ce ya yanke shawarar shirya taron ne domin ya gode wa Allah a kan rayuwarsa da ta ’yan uwa.

 

Ya kuma yabawa Gwamna Abdullahi Sule da sarakunan gargajiya da masu ruwa da tsaki da sauran jama’a bisa goyon bayan da suke ba shi don samun nasara.

 

Basaraken ya yi amfani da wannan damar wajen tabbatar da aniyarsa na inganta hadin kai da zaman lafiya a tsakanin talakawansa.

 

COV/Aliyu Muraki/Lafia./Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sarakuna Shekara zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Katsina Ta Ƙaddamar Da Shirin Tallafin Abinci Na Naira Biliyan 4

Shirin Rumbun Saukin zai fi bayar da da muhimmanci ne kan ma’aikatan gwamnati da dattijai masu shekaru 60 zuwa sama, inda kayan abincin za su kasance a nau’ikan ma’aunai daban-daban domin a dai-daita da bukatun iyalai da samun masu cin gajiya wanda za su yi rijista ta yanar gizo ko kuma ta cibiyoyin da aka tanada domin shirin.

 

Danja, ya ƙara da cewa burin gwamnati shi ne faɗaɗa shirin zuwa dukkan ƙananan hukumomi 34 da ke jihar, tare jaddada himmatuwar gwamnatin Katsina na ci gaba da ɗaukar nauyin shirin domin rage matsin tattalin arziki da jama’a ke fuskanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250
  • Kwastam Da Hukumar NPA Sun Kulla Hadakar Bunkasa Ingancin Aiki A Tashoshin Jiragen Ruwa
  • GORON JUMA’A
  • Jigawa Ta Kebe Wuraren 57 don Kare Rikicin Manoma da Makiyaya
  • An Fara Tattaunawa Tsakanin Isra’ila Da Hamas Kan Mataki Na Gaba Na Tsagaita Wuta
  • Iran Ta Yi Tir Da Kakkausar Murya Kan Barazanar Soji Da Isra’ila Ke Yi Mata
  • Helikwaftan farko ƙirar Najeriya zai fara aiki —NASENI
  • Hajji: An Bukaci Gwamnoni Da Su Gyara Sansanin Alhazai A Jihohinsu
  • Al’umma Sun Nuna Alhininsu Kan Takaddamar Akpabio Da Sanata Natasha
  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙaddamar Da Shirin Tallafin Abinci Na Naira Biliyan 4