Rundunar Sojin Najeriya ta 8 da ke Sokoto ta bayyana ayyukanta na zamantakewar jama’a na yammacin Afirka WASA, a matsayin muhimmin kayan aiki don wanzar da hadin kai da ci gaba a yankin yammacin Afirka.

 

Babban Kwamandan Rundunar, Manjo Janar Ibikunle Ajose ya bayyana haka a wajen taron na bana da aka gudanar a Bataliya ta 26 dake jihar Sokoto.

 

Ajose ya ce hukumar ta WASA tana baiwa hafsoshi da sojoji da iyalansu damar yin mu’amala cikin yanayi mai kyau.

 

Ya bayyana cewa, tarihin wannan biki ya samo asali ne tun a shekarar 1901, a lokacin shigar da Najeriya cikin rundunar sojojin kasashen yammacin Afrika, saboda al’adu daban-daban na sojojin kasashen yammacin Afirka, shi yasa mahukunta a wancan lokaci suka gabatar da WASA duk shekara domin sojoji su shiga.

 

Kwamandan ya yi nuni da cewa zaman lafiya da hadin kai da ake samu a cikin sojojin Najeriya sakamakon manufofin WASA ne a yankin yammacin Afirka.

 

Manjo Janar Ibikunle Ajose ya kuma duba irin nasarorin da rundunar ta samu kan yaki da ‘yan bindiga da sauran tashe-tashen hankula da ke faruwa a yankin Arewa maso Yamma .

 

Ya ce, a shekarar 2024, rundunar ta samu nasarar gudanar da ayyukanta na yaki da ayyukan bata gari a duk fadin Nijeriya.

 

Ya ce nasarorin da aka samu sun hada da kaddamar da runduna ta 248 ta Recce a Illelah, da tura babban hafsan soji na musamman na Bataliya ta 7 a karamar hukumar Gudu a jihar Sokoto da kaddamar da sabbin kayan aiki na sojojin sama da sauran makaman yaki a Sokoto.

 

A cewarsa, abubuwan da suka faru sun haifar da nasarori da dama a ayyukan sojoji na fadin yanki na 8.

 

A nasa jawabin, gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, wanda ya samu wakilcin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin sana’o’i da tsaro, Kanar Ahmed Usman mai ritaya, ya yabawa kokarin rundunar na ci gaba da kulla alaka mai karfi da al’adunsu.

 

Aliyu ya ce bikin ya zama abin tunatarwa ne kan alhakin da ya rataya a wuyansu na bunkasa fahimtar juna, mutunta juna, da hadin kai a tsakanin kungiyoyi da al’ummomi daban-daban a yammacin Afirka.

 

NASIR MALALI/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: wasa yammacin Afirka

এছাড়াও পড়ুন:

GORON JUMA’A

Sako daga Alawiyya Jilani Jihar Kano:

Ina gaishe da Mummy da Abba, da kannena Zuhra, Sajida, Alhaji, da dukkanin kawayena na islamiyya dana boko wadanda muka kammala dukka, ina gaida Khadija (Sweet Bala), ina gaishe da Siyama Abdul, ina gaishe da Aunty Hajara da sauran ‘yan’uwa da fatan sakon ya iso gare ku kuma da fatan kun yi juma’a lafiya.

Sako daga Balaraba Ibrahim Jihar Kaduna:

Assalam.. Dan Allah a gaishe mun da Sisi ‘yar fucika uwar tsokana, da Hajiya Hazira, da Aunty Amina mai sakwara, ina gaishe da baby nice, da Binta kwaram da sauran wadanda ban gaisar ba wanda suka sanni.

Sako daga Yusuf Uba Muhammad Jihar Kano:

Haj. Rabi’at dan Allah a mikan sakon gaisuwata zuwa ga Baffa Salisu da abokaina kamar su; Zayyanu, Hassan, Fatuhu, Mansur, Aliyu dan ball, su Idris, Shafi’u dake garin Katsina, Alkhairin Allah ya kai masa, sannan ina gaishe da budurwata Maryam Baby, Allah ya sa ta yi juma’a lafiya.

Sako daga Bilyaminu Ahmad Jihar Kaduna:

Sakona zuwa ga dukkanin al’ummar musulmi ne na fadin duniya, ina gaishe da kowa kuma ina yi mana addu’ar fara azumi lafiya mu gama lafiya dan isar Annabi da alkur’ani.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Nabamamu a Zamfara
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara
  • GORON JUMA’A
  • Amnesty: Isra’ila Ta Kori Falasdinawa 40,000 Daga Yammacin Kogin Jordan
  • Shugaban Hafsan Sojan Sama Na Najeriya Ya Zama Shugaban Kungiyar Sojojin Sama Na Afrika
  • Majalisar Dattijan Aljeriya Ta Soke Duk Wata Hulda Da Majalisar Dattijan Faransa
  • Sojojin Iran Sun Kammala Atisayen Zulfikar 1403 Da Faretin Sojojin Ruwa
  • Shugabannin Afirka Ta Kudu, Malaysia Da Colombia Sun Yi Kira Da A Kawo Karshen Laifukan Isra’ila
  • Sanata Natasha na neman diyyar N100bn wurin Akpabio
  • Nebenzia : Hare-haren Sojojin Isra’ila a Lebanon da Syria na kara dagula lamura a yankin