Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-01@14:05:27 GMT

Saura Kiris Mu Kai Ga Bello Turji – Rundunar Sojan Nijeriya

Published: 27th, January 2025 GMT

Saura Kiris Mu Kai Ga Bello Turji – Rundunar Sojan Nijeriya

Kwamandan runduna ta 1 ta sojojin Najeriya Gusau, Birgediya Janar Opurum Timothy, ya baiwa al’ummar jihar Zamfara aniyar rundunar sojojin Najeriya wajen ci gaba da aiki tukuru domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

 

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a karshen taron rundunar sojojin Najeriya ta yammacin Afirka WASA 2024 da aka gudanar a Gusau.

 

Kungiyar WASA wani taron ne na shekara-shekara da rundunar sojojin Najeriya ke shiryawa domin murnar dimbin al’adun gargajiya na wannan kasa mai girma.

 

Taron na shekara-shekara yana tattaro Jami’ai, Sojoji, da iyalansu a cikin annashuwa don bikin da kuma nuna ƙarshen ayyukan shekara.

 

Janar Opurum wanda ya jaddada kudirin rundunar na kawar da ‘yan fashi daji da kuma dawo da zaman lafiya a Zamfara da yankin Arewa maso Yamma gaba daya, ya yi kira ga sojojin da su jajirce wajen gudanar da ayyukansu, yana mai jaddada cewa, sadaukarwarsu na da matukar muhimmanci wajen samun zaman lafiya mai dorewa.

 

A cewarsa, a halin yanzu fitaccen jagoran ‘yan bindigar Bello Turji na kan hanyarsa ta zuwa lahira saboda hare-haren da sojoji ke kai wa a jihar Zamfara.

 

“Bello Turji matsoraci ne kuma ya yi watsi dadakarunsa saboda matsin lamba da muka yi masa. Mun share da yawa daga cikinsu kuma za mu ci gaba da ci gaba da kai farmakin kai tsaye zuwa maboyarsu.”

 

Kwamandan Birgediya wanda ake yi wa lakabi da “Jar Kunama”, ya yabawa al’ummar Zamfara bisa yadda suke ba da hadin kai, musamman ta hanyar samar da muhimman bayanan sirri, wanda ya haifar da gagarumar nasara.

 

Tun da farko, Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara, wanda kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Meriga ya wakilta, ya yabawa rundunar sojojin Najeriya da sauran jami’an tsaro bisa namijin kokarin da suke yi na samar da zaman lafiya mai dorewa a fadin jihar ta Zamfara.

 

Taron WASA na bana a Gusau ya samu halartar manyan baki da suka hada da sarakunan gargajiya da shugabannin sauran hukumomin tsaro kamar rundunar sojojin saman Najeriya da jami’an tsaro da dai sauransu.

 

Muhimman abubuwan da suka faru a wajen taron sun hada da yawon shakatawa, baje kolin al’adu da raye-raye, wasan taekwondo, tuggun yaki, da kunna wuta da Kwamandan Brigade ya yi da dai sauransu.

 

Yayin da wasu da dama da suka yi nasara suka je gida da kyaututtuka daban-daban.

 

COV/AMINU DALHATU/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: wasa Zamfara rundunar sojojin Najeriya zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Halin jama’a za su shiga idan Kamfanin Kaduna Electric ya ki sauraren ma’aikatansa?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Wutar lantarki a Najeriya ta zama ginshiƙin rayuwa da al’umma ba sa iya rayuwa ba tare da ita ba. A duk lokacin da aka ɗauke ta al’umma kan shiga matsanancin hali.

Mutane da dama sun dogara ne da wutar lantarki wajen tafiyar da harkokinsu na yau da kullum, kai har ma da na kasuwanci.

A kwanakin baya ne jihohin Kaduna, Sakkwato, Zamfara da kuma Kebbi suka fuskanci ɗaukewar wutar lantarki na tsawon kwanaki, wanda ya jefa al’ummar jihohi cikin halin ni-’yasu.

NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi? DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan halin da al’ummar jihohin da ke ƙarƙashin kulawar kamfanin rarraba wuta na Kaduna Electric za su shiga idan ma’aikatan kamfanin suka shiga yajin aiki.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ramadan: ’Yan sanda sun tsaurara tsaro saboda azumi a Borno
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Nabamamu a Zamfara
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu a Zamfara
  • Buhari ya koma Kaduna da zama bayan shafe shekara 2 a Daura
  • Sojojin Nijeriya Za Su Fara Karɓar N3,000 Kudin Abinci A Rana
  • Shugaban Hafsan Sojan Sama Na Najeriya Ya Zama Shugaban Kungiyar Sojojin Sama Na Afrika
  • NAJERIYA A YAU: Halin da jama’a za su shiga idan Kamfanin Kaduna Electric ya ƙi sauraren ma’aikatansa?
  • NAJERIYA A YAU: Halin jama’a za su shiga idan Kamfanin Kaduna Electric ya ki sauraren ma’aikatansa?
  • Gwamnatin Jigawa Ta Biya  Sama Da Naira Miliyan 730 Ga Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya
  • Sojojin Iran Sun Kammala Atisayen Zulfikar 1403 Da Faretin Sojojin Ruwa