HausaTv:
2025-03-31@12:50:35 GMT

Jagoran Kungiyar Ansarullah Ta Yemen Ya Shirin Na Tunkarar Harin Amurka

Published: 27th, January 2025 GMT

Jagoran kungiyar Ansarullah ya bayyana cewa: A shirye suke su tunkari duk wani harin Amurka kuma ya gargadin sojojin haya

Jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyed Abdul-Malik Badruddeen al-Houthi ya tabbatar da cewa: Amurka ta yi amfani da dukkan karfinta wajen tallafawa haramtacciyar kasar Isra’ila da kuma kokarin murkushe al’ummar Falasdinu, yana mai jaddada tsayin daka da matsayarsa da ke tafiya a kan tubalin gaskiya, ikhlasi da ke gudana a tsakanin al’ummar Falastinu da ‘yan gwagwarmayarsu.

Sayyid Abdul-Malik Badruddeen al-Houthi ya bayyana a yayin zagayowar ranar shahadar Sayyid Hussein Badruddeen al-Houthi, cewa: Abin da hukumomi suka yi a shekara ta 2004 kan shahidi wanda shi ne ya kafa tattakin Alkur’ani, kuma shugaba shahidi Hussein Adwan, ba a yi adalci ba, yana mai nuni da cewa abin da shahidin Alkur’ani ya yi shi ne koyar da tarbiyyar Alkur’ani, da kalubalantar masu girman kai da kuma kauracewa kayayyakin Amurka da Haramtaciyyar kasar Isra’il kan matakin da suka dauka na kaddamar da hare-haren wuce gona kan al’ummar kasarsu.

Ya kara da cewa, bayan abubuwan da suka faru a ranar 11 ga watan Satumba, Amurka ta yi shirin mayar da ita tamkar wata kafa ta wani gagarumin yakin neman zabe na tsaurara iko a kan al’ummar kasar, da mamaye yankunanta da kuma kawar da asalinta, ya ci gaba da cewa gwamnatocin da suka mika wuya ga Amurka kuma an bude dukkan kofofin zuwa gare ta, ciki har da gwamnatin Yemen a karkashin taken kawancen yaki da ta’addanci, inda gwamnati a Yemen bayan a abubuwan da suka faru na ranar 11 ga watan Satumba suka bude hanya ga Amurka a cikin soja, tsaro, tattalin arziki, ilimi, kafofin watsa labaru da kuma maganganun addini.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe mutum 10 a wani sabon hari a Filato

Aƙalla mutum 10 ne suka rasu, yayin da wasu uku suka jikkata sakamakon harin da wasu mahara suka kai wa al’ummar Ruwi da ke Ƙaramar Hukumar Bokkos, a Jihar Filato.

Maharan sun kai harin ne a daren ranar Alhamis, inda suka buɗe wuta kan mutanen da suka halarci wata jana’iza da misalin ƙarfe 9:30 na dare.

’Yan sanda sun haramta hawan Sallah a Kano An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara

Wani mazaunin yankin ya ce: “Mummunan hari ne. Sun zo kwatsam suka fara harbi. Muna roƙon hukumomin tsaro da su ɗauki mataki don kare al’ummarmu.”

Rundunar ’yan sandan jihar, ta tabbatar da faruwar harin, amma ba ta bayyana adadin waɗanda suka rasu ba.

Kakakin rundunar, DSP Alabo Alfred, ya ce, “Kwamishinan ‘yan sanda ya tura ƙarin jami’an tsaro da kayan aiki don wanzar da zaman lafiya.

“Za mu tabbatar da cewa waɗanda suka aikata wannan aika-aika sun fuskanci hukunci.”

Gwamnatin Jihar Filato ta yi Allah-wadai da harin.

Kwamishiniyar Yaɗa Labarai ta jihar, Joyce Ramnap, ta tabbatar wa jama’a cewa ana ɗaukar matakan kawo ƙarshen irin waɗannan hare-hare.

“Gwamnati ba za ta lamunci kashe rayukan ‘yan ƙasa ba. An umarci hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki tare da tabbatar da cewa sun fuskanci hukunci.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  •  Janar Sari: Sojojinmu Sun Yi Taho Mu Gama Da Amurkawa Sau 3 A Cikin Sa’o’i 24
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Hamas ta yi Tir da kakkausar murya da harin Isra’ila kan masu aikin ceto a Gaza
  • Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya
  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  • An kashe mutum 10 a wani sabon hari a Filato
  • Sharhi: Taruka Da Gangamin Ranar Quds Ta Duniya 2025
  • Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya