Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kera Sabon Jirgin Sama Mara Matuki Ciki
Published: 27th, January 2025 GMT
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun kera wani jirgi maras matuki ciki mafi girman da suka Sanya masa suna “Gaza”
A jiya Lahadi, a gefen atisayen soji mai taken “Manzon Allah Mai Girma na 19” da aka gudanar da gwajin makamansu, sun samu nasarar gwajin sabon jirgin sama maras matuki ciki mai suna “Gaza” wanda ake daukansa a matsayi mafi girman jirgin saman maras matuki ciki da zai iya yin luguden wuta mafi girma da tsanani, jirgin yana cin dogon zango kuma shi ne mafi girma da Iran ta kera wajen kai farmakin da zai jefa bama-bamai 8 akan wurare 8 a kasa.
Jirgin Gaza maras matuki (wanda ake kira Shahed 149) shi ne jirgi mara matuki mafi tsayi da Iran ta kera kuma an bayyana shi a shekara ta 2021. Wannan jirgi mara matuki mai nauyi da ya kai tsawon mita 21, kuma yana iya shawagi har tsawon sa’o’i 35. kuma rufin jirgin ya kai kilomita 10/5, gudunsa ya kai km 35 a cikin sa’a guda, sannan yana iya daukar bama-bamai da ya kai nauyin kilogiram 500, kuma karfin tafiyarsa ya fi na Shahed 129 maras nauyi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: maras matuki
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mutum 10 a wani sabon hari a Filato
Aƙalla mutum 10 ne suka rasu, yayin da wasu uku suka jikkata sakamakon harin da wasu mahara suka kai wa al’ummar Ruwi da ke Ƙaramar Hukumar Bokkos, a Jihar Filato.
Maharan sun kai harin ne a daren ranar Alhamis, inda suka buɗe wuta kan mutanen da suka halarci wata jana’iza da misalin ƙarfe 9:30 na dare.
’Yan sanda sun haramta hawan Sallah a Kano An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a ZamfaraWani mazaunin yankin ya ce: “Mummunan hari ne. Sun zo kwatsam suka fara harbi. Muna roƙon hukumomin tsaro da su ɗauki mataki don kare al’ummarmu.”
Rundunar ’yan sandan jihar, ta tabbatar da faruwar harin, amma ba ta bayyana adadin waɗanda suka rasu ba.
Kakakin rundunar, DSP Alabo Alfred, ya ce, “Kwamishinan ‘yan sanda ya tura ƙarin jami’an tsaro da kayan aiki don wanzar da zaman lafiya.
“Za mu tabbatar da cewa waɗanda suka aikata wannan aika-aika sun fuskanci hukunci.”
Gwamnatin Jihar Filato ta yi Allah-wadai da harin.
Kwamishiniyar Yaɗa Labarai ta jihar, Joyce Ramnap, ta tabbatar wa jama’a cewa ana ɗaukar matakan kawo ƙarshen irin waɗannan hare-hare.
“Gwamnati ba za ta lamunci kashe rayukan ‘yan ƙasa ba. An umarci hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki tare da tabbatar da cewa sun fuskanci hukunci.”