HausaTv:
2025-03-01@14:32:38 GMT

Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kera Sabon Jirgin Sama Mara Matuki Ciki

Published: 27th, January 2025 GMT

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun kera wani jirgi maras matuki ciki mafi girman da suka Sanya masa suna “Gaza”

A jiya Lahadi, a gefen atisayen soji mai taken “Manzon Allah Mai Girma na 19” da aka gudanar da gwajin makamansu, sun samu nasarar gwajin sabon jirgin sama maras matuki ciki mai suna “Gaza” wanda ake daukansa a matsayi mafi girman jirgin saman maras matuki ciki da zai iya yin luguden wuta mafi girma da tsanani, jirgin yana cin dogon zango kuma shi ne mafi girma da Iran ta kera wajen kai farmakin da zai jefa bama-bamai 8 akan wurare 8 a kasa.

Jirgin Gaza maras matuki (wanda ake kira Shahed 149) shi ne jirgi mara matuki mafi tsayi da Iran ta kera kuma an bayyana shi a shekara ta 2021. Wannan jirgi mara matuki mai nauyi da ya kai tsawon mita 21, kuma yana iya shawagi har tsawon sa’o’i 35. kuma rufin jirgin ya kai kilomita 10/5, gudunsa ya kai km 35 a cikin sa’a guda, sannan yana iya daukar bama-bamai da ya kai nauyin kilogiram 500, kuma karfin tafiyarsa ya fi na Shahed 129 maras nauyi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: maras matuki

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Halin jama’a za su shiga idan Kamfanin Kaduna Electric ya ki sauraren ma’aikatansa?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Wutar lantarki a Najeriya ta zama ginshiƙin rayuwa da al’umma ba sa iya rayuwa ba tare da ita ba. A duk lokacin da aka ɗauke ta al’umma kan shiga matsanancin hali.

Mutane da dama sun dogara ne da wutar lantarki wajen tafiyar da harkokinsu na yau da kullum, kai har ma da na kasuwanci.

A kwanakin baya ne jihohin Kaduna, Sakkwato, Zamfara da kuma Kebbi suka fuskanci ɗaukewar wutar lantarki na tsawon kwanaki, wanda ya jefa al’ummar jihohi cikin halin ni-’yasu.

NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi? DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan halin da al’ummar jihohin da ke ƙarƙashin kulawar kamfanin rarraba wuta na Kaduna Electric za su shiga idan ma’aikatan kamfanin suka shiga yajin aiki.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAHCON Ta Naɗa Sabon Sakatare
  • Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa
  • LEADERSHIP HAUSA Ta Bayyana Wadanda Suka Yi Nasara A Gasar Gajerun Labaran Soyayya
  • Me Sabon Karfin Samar Da Ci Gaban Ayyukan Gona Zai Kawo Mana?
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ƙirar Nijeriya Zai Fara Tashi – NASENI
  • Shugaban Hafsan Sojan Sama Na Najeriya Ya Zama Shugaban Kungiyar Sojojin Sama Na Afrika
  • NAJERIYA A YAU: Halin da jama’a za su shiga idan Kamfanin Kaduna Electric ya ƙi sauraren ma’aikatansa?
  • NAJERIYA A YAU: Halin jama’a za su shiga idan Kamfanin Kaduna Electric ya ki sauraren ma’aikatansa?
  • Gwamnatin Jigawa Ta Biya  Sama Da Naira Miliyan 730 Ga Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya
  • Iran Ta Kaddamar Da Kayakin Aiki Na Samar Da Maganin Wata Nau’in Cutar Cancer Ko Daji