Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-20@23:28:27 GMT

An Yabawa Darikar Tijjaniyya akan Samar da Hadin kai a Najeriya.

Published: 27th, January 2025 GMT

An Yabawa Darikar Tijjaniyya akan Samar da Hadin kai a Najeriya.

Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima, ya yaba da irin gudunmawar da darikar Tijjaniyya ke bayarwa wajen samar da hadin kai a tsakanin al’ummar musulmin kasar nan.

 

Mataimakin shugaban kasar ya yi wannan yabon ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron Mauludin bana 2025 na marigayi Sheikh Ibrahim Nyass, jagoran darikar Tijjaniyya a filin wasa na Sani Abacha dake Kano.

 

Mataimakin wanda ya samu wakilcin Alhaji Babagana Fannami, Ya yabawa kungiyar musulmi bisa tsayin daka a tsawon karnukan da suka gabata akan koyarwar addinin musulunci na gaskiya.

 

Shettima wanda shi ne babban bako na musamman a wajen taron, ya yaba da tsarin jagoranci na darikar ‘Sufi’ ga bil’adama.

 

Babban bako na musamman ya jaddada irin tsayin dakan da darikar Tijjaniyya ke da shi wajen koyi da darussan rayuwan Annabi Muhammad ba tare da tauye lamuran fikihu na Musulunci ba.

 

Don haka ya tunatar da musulmi da su yi koyi da koyarwa ta gaskiya ta Musulunci, su guje wa tsatsauran ra’ayi.

 

Hakazalika babban mai masaukin baki Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya yaba da kokarin Darikar Tijjaniyya wajen wanzar da zaman lafiya da zumunci da sauran kungiyoyin a Najeriya.

 

“A matsayina na mai masaukin baki, dole ne mu yaba muku da kuka zo Kano daga nesa da kusa domin halartar mauludin bana na Sheik Ibrahim Nyass.”

 

Mai Martaba Sarkin Kano na 16 Khalifa Dr. Muhammadu Sanusi II, ya yi addu’ar samun hadin kan musulmin duniya baki daya da kuma hakuri da sauran mabiya addinai.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taro Tijaniyya

এছাড়াও পড়ুন:

An Rantsar Da Shugabanin Kungiyar KekeNapep A Kaduna

 

Kungiyar Masu Babura Uku ta Najeriya, Jihar Kaduna ta Rantsar da Shugabannin Sassa Goma Sha Biyar da Manyan Jami’ansu don Gudanar da Harkokin Kungiyar a Tsawon Shekaru Hudu Masu Zuwa.

 

Mataimakin Kwamandan Hanya kuma Mataimakin Jami’in Wayar da Kai na Hukumar Kiyaye Haddura ta Tarayya (FRSC), Kaduna, Usman Garba, wanda ya yi magana da manema labarai bayan bikin rantsarwa, ya yaba wa kungiyar, yana mai cewa wannan ci gaba ne mai kyau ga kungiyar.

 

Ya ce Hukumar Kiyaye Haddura na farin ciki da wannan ci gaba saboda sabon tsarin shugabanci zai taimaka wajen magance matsalolin da suka shafi direbobin babura uku (Keke Napep) da hukumar ke fuskanta a jihar.

 

A cewarsa, yanzu hukumar za ta yi aiki kafada da kafada da kungiyar wajen horas da mambobinta kan amfani da hanyoyin mota da kuma basu ilimi na musamman lokaci zuwa lokaci domin su san yadda za su yi amfani da hanyoyin jama’a yadda ya kamata.

 

A nasa jawabin, Shugaban Kungiyar Masu Babura Uku ta Najeriya, Jihar Kaduna, Kwamared Jacob Ayuka, ya bayyana cewa kungiyar na taka muhimmiyar rawa a harkar sufuri ta Najeriya.

 

Ya bayyana cewa, tare da karfi a matakin tushe da kuma samun karbuwa a kasa baki daya, kungiyar na ci gaba da fafutukar ganin an samu ingantattun dokoki, da karfafa wa mambobinta gwiwa, tare da bada gudunmawa ga ci gaban tattalin arzikin Najeriya.

 

Kwamared Ayuka ya kara da cewa kungiyar na aiki a matsayin kungiya mai tsari, ba mai neman riba ba, wacce ke kokarin tallafa wa mambobinta ta hanyar fafutuka, shirye-shiryen jin kai, tallafin aiki, da kuma hadin gwiwa da hukumomin gwamnati da hukumomin sufuri.

 

An rantsar da shugabannin sassa goma sha biyar da jami’ansu bayan gudanar da zabe, kuma an mikawa kowane shugaban sashi takardar shaida ta nasara.

 

Daga cikin shugabannin da aka rantsar akwai:

 

Sashin Wusili – Kwamared James Ibrahim Yakubu;

 

Unguwan Mu’azu – Kwamared Mustapha Aliyu;

 

Urban Shelter – Kwamared Shehu Lawal;

 

Kasuwar Sabo – Kwamared Emmanuel Okiki John;

 

Rain Oil – Kwamared Jacob Ayuka.

 

Sauran su ne:

 

Tashar ‘Yan sanda Tsohuwar – Kwamared Paul Dogo;

 

Rukunin Narayi Junction – Kwamared Tanimu Mohammed;

 

Jami’ar KASU – Kwamared Sani Adam;

 

Kongo, Zaria – Aminu Ibrahima.

 

Kana kuma:

 

Jan-Ruwa – Kwamared Patrick A. Sanda;

 

Hayin Mal Bello – Kwamared Abubakar Ilyasu;

 

FCE Zaria – Kwamared Isyaka Baba Tanko;

 

Charity – Kwamared Jatau Ango Manga;

 

Bakin-Ruwa – Kwamared Mahadi Lawan;

 

AP Maraban Rido – Kwamared Livinus Solomon.

 

Mataimakin Kwamandan Hanya kuma Mataimakin Jami’in Wayar da Kai na FRSC Kaduna, Usman Garba, na mika takardar shaida ga daya daga cikin shugabannin sassan a yayin bikin.

 

A nasa bangaren, shugaban sashin Kasuwar Sabo, Kwamared Emmanuel Okiki John, ya bayyana cewa sashin kasuwa ne mai cike da aiki, wanda ke da korafe-korafe da dama, kuma akwai shirin da aka tanadar don gyara lamura.

 

Kwamared John ya sha alwashin yin aiki tukuru tare da sauran shugabanni don amfanin da ci gaban mambobin kungiyar.

 

Cov/ Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Rantsar Da Shugabanin Kungiyar KekeNapep A Kaduna
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yaba Da Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka Zagaye Na Biyu A Birnin Roma
  • Kada Kanawa su bari rigingimun siyasa su hana su zaman lafiya — Shettima
  • Ka Da Ku Bari Siyasa Ta Raba Ku – Shettima Ga ’Yan Siyasar Kano
  • Kada Ku Bari Siyasa Ta Raba Ku – Shettima Ga ’Yan Siyasar Kano
  • Babu wanda ya hana Shettima shiga Aso Rock ba— Fadar Shugaban Ƙasa
  • Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima
  • Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka
  • Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu  
  • BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano