HausaTv:
2025-03-31@15:27:22 GMT

Belarus : Alexander Lukashenko Ya Sake Zaben Shugaban Kasa A Karo Na 7

Published: 27th, January 2025 GMT

Sakamakon farko na zaben shugaban kasa da babbar hukumar zaben kasar Belarus ta fitar da jijjifin safiyar yau Litinin ya nuna cewa, Alexander Lukashenko ne ya lashe zaben, inda ya samu kashi 86.82 cikin dari na adadin kuri’un da aka kada.

A bisa dokar kasar ta Belarus dai, ana ayyana duk dan takarar shugaban kasa da ya samu fiye da kashi 50 cikin dari na kuri’un da aka kada a matsayin wanda ya yi nasara

Hakan na nufinb Mista Lukashenko zai jagoranci kasar a wani wa’adi na mulki na bakwai na shekaru biyar.

Hukumar zaben ta sanar da fitowar kashi 81.5% na ‘yan kasar miliyan 6.9 da suka fito rumfunan zabe.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Abin da ya sa nake jin daɗin yadda Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa — Buhari

Tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa yana jin daɗin yadda shugaban ƙasar Bola Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa.

Buhari ya ce har yanzu Tinubu bai sauya ba daga tsari da manufofin da jam’iyyar APC ta kafa wanda har ya sanya shi kansa ’yan Nijeriya suka zaɓe shi a 2015.

An ga watan Sallah a Saudiyya Dalilin da Aminu Bayero ba zai iya jagorantar hawan Sallah ba — Kurawa

Buhari ya bayyana hakan a saƙonsa na taya Tinubu murnar zagayowar ranar haihuwarsa, wanda ya cika shekaru 73 a doron ƙasa.

Sanarwar da mai magana da yawun Buhari, Mallam Garba Shehu ya fitar a ranar Asabar, ta ce tsohon shugaban yana alfahari da alaƙarsa da shugaban ƙasar na yanzu.

Sanarwar ta ce Buhari da Tinubu sun gana ta wayar tarho a ranar Juma’a, inda a ciki Buhari ya yi Tinubu addu’ar tsawon rai da ingantacciyar lafiya da, sannan ya yi masa fatan samun nasarar a mulkinsa.

“Idan muka yi wa shugabanninmu addu’a, muna yi wa kanmu ne. Ƙasarmu na buƙatar addu’o’inmu,” in ji Buhari a ganawarsa da Tinubu.

Buhari ya ce shi da iyalansa suna godiya ga Tinubu da sauran jagororin jam’iyyar bisa ƙoƙarin da suka yi wajen kafa jam’iyyar APC, inda har ya samu nasarar zama shugaban ƙasa har sau biyu, bayan ya sha gwadawa a baya ba tare da samun nasara ba.

“Lokacin da ’yan Nijeriya suka zaɓi APC a 2023, zaɓi suka yi domin kafa tubalin sabuwar Nijeriya inda talakawa za su samu damarmakin da suke buƙata, kuma ina jin daɗi har yanzu ba a kauce daga tsarin ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Girgizar Kasa: Shugaban Kasar Myanmar Ya Mika Godiya Ga Tawagar Likitocin Yunnan Ta Kasar Sin
  • Karamar Hukumar Jahun Ta Karrama Hakimai Da Limamai Da Kayan Sallah
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Fiji: Ya Kamata A Koyi Fasahohin Da Kasar Sin Ta Samu A Fannin Raya Kasa
  • Abin da ya sa nake jin daɗin yadda Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa — Buhari
  • Shugaba Xi Ya Jajantawa Shugaban Myanmar Game Da Girgizar Kasar Da Ta Auku
  • Rikici Ya Turnuke Jam’iyyar SDP A Yayin Da Aka Samu Shugabanni Bangare Biyu A Kogi
  • Gwamnati Ta Ba da Umarnin Tafiya Yi Wa Ƙasa Hidima Ga Duk Masu HND
  •  Iran Ta Yi Allawadai Da Sabon Harin HKI A Kasar Lebanon
  • Shugaban CMG Ya Gana Da Ministar Raya Al’adu Ta Rasha
  • Xi Jinping Ya Gana Da Wakilan Masana’antu Da Cinikayya Na Kasa Da Kasa