Belarus : Alexander Lukashenko Ya Sake Zaben Shugaban Kasa A Karo Na 7
Published: 27th, January 2025 GMT
Sakamakon farko na zaben shugaban kasa da babbar hukumar zaben kasar Belarus ta fitar da jijjifin safiyar yau Litinin ya nuna cewa, Alexander Lukashenko ne ya lashe zaben, inda ya samu kashi 86.82 cikin dari na adadin kuri’un da aka kada.
A bisa dokar kasar ta Belarus dai, ana ayyana duk dan takarar shugaban kasa da ya samu fiye da kashi 50 cikin dari na kuri’un da aka kada a matsayin wanda ya yi nasara
Hakan na nufinb Mista Lukashenko zai jagoranci kasar a wani wa’adi na mulki na bakwai na shekaru biyar.
Hukumar zaben ta sanar da fitowar kashi 81.5% na ‘yan kasar miliyan 6.9 da suka fito rumfunan zabe.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Al’umma Sun Nuna Alhininsu Kan Takaddamar Akpabio Da Sanata Natasha
An shawarci majalisar dokokin kasar da su mai da hankali kan ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin kasar nan domin inganta shugabanci nagari.
Masu kiran waya a shirin “KAKAKI” na gidan Rediyon Najeriya Karama FM ne suka bada shawarar hakan a lokacin da suke ba da tasu gudunmawar a kan batutuwan da suka shafi kasa.
Sun bayyana damuwarsu kan rahotannin karar da wata sanata daga jihar Kogi, Natasha Akpoti, ta shigar kan shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, biyo bayan zargin bata suna.
Alhaji Ibrahim Alaramma, Idris Adamu Danfulani, da Sani Batira sun jaddada bukatar shugabannin majalisar su tabbatar da kafa doka mai inganci don yaki da talauci da rashin tsaro.
Shi ma da yake jawabi, wani bako a shirin, Alhaji Suleiman Muhammad ya yi kira ga gwamnati da ta kara samar da ayyukan raya kasa da ababen more rayuwa kamar yadda ake yi a kasashen da suka ci gaba.
Suleiman Kaura