Shugaban kasar Kenya William Ruto a wata sanarwa da ya fitar ya sanar da cewa, zai gudanar da wani babban taro na musamman na kungiyar kasashen gabashin Afirka EAC a cikin sa’o’i 48 masu zuwa tare da halartar shugaban kasar Congo Félix Tshisekedi da shugaban Rwanda Paul Kagame.

Taron dai na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan tawayen M23 ke ci gaba da dannawa kan birnin Goma inda ake ta musayar wuta.

A cewar wasu majiyoyin MDD da na tsaro, sojojin Rwanda da mayakan M23 sun shiga birnin a ranar Lahadi, in ji kamfanin dillancin labaran Faransa.

Yakin da ake gwabzawa a kusa da Goma da kuma harbe-harbe da aka yi a birnin ya kuma sa mazauna babban birnin lardin ketare kan iyaka zuwa kasar Rwanda.

A wani labarin kuma sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya zargi gwamnatin Kigali kan sabon fadan da akeyi a gabashin DRC.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kwarewar Kasar Sin Da Ci Gabanta A Fannin Fasaha Na Da Muhimmanci Wajen Inganta Zamanantar Da Afirka

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  • Girgizar Kasa: Shugaban Kasar Myanmar Ya Mika Godiya Ga Tawagar Likitocin Yunnan Ta Kasar Sin
  • Kashe Matafiya: Gwamnatin Kano Ta Aika Tawaga Zuwa Edo
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne
  • Wani Jami’in Leken Asirin HKI Ya Bukaci Kasashen Afirka Su Taimaka Su Karmi Falasdinawan Da Za;a Kora Daga Gaza
  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  • MDD Ta Yi Gargadi Akan Mummunan Yanayin A Sudan Ta Kudu
  • Taron Boao Ya Sake Ba Duniya Damar Ganin Abubuwa Masu Jan Hankali Game Da Sin
  • Kwarewar Kasar Sin Da Ci Gabanta A Fannin Fasaha Na Da Muhimmanci Wajen Inganta Zamanantar Da Afirka