An Tsawaita Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsakanin Isra’ila Da Lebanon Har Zuwa 18 Ga Watan Fabrairu
Published: 27th, January 2025 GMT
An tsawaita yarjejeniyar tsagaita bude wuta tsakanin Isra’ila da Lebanon na tsawon kimanin makonni uku bayan da gwamnatin kasar ta ki janye dakarunta kamar yadda aka kulla da farko.
An bayyana cewa yarjejeniyar tsakanin kasashen biyu za ta ci gaba da aiki har zuwa ranar 18 ga Fabrairu, 2025.
Shi ma firaministan kasar Labanon Najib Mikati ya tabbatar da tsawaita wa’adin, yana mai kara da cewa Lebanon za ta mutunta hakan.
Bisa yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka sanar tsakanin Isra’ila da Hizbullah a watan Nuwamba, a jiya ne ya kamata sojojin Isra’ila su fice daga kudancin Lebanon.
“Gwamnatin Lebanon ta sake jaddada aniyarta ta ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta har zuwa ranar 18 ga Fabrairu, 2025,” in ji Mikati a cikin wata sanarwa, a cewar kamfanin dillancin labarai na AFP.
Duk da haka a ranar Lahadi sojojin Isra’ila sun bude wuta kan al’ummar Lebanon da ke kokarin komawa gidajensu a kudancin kasar, inda suka kashe fararen hula akalla 22 tare da jikkata wasu fiye da 120 na daban.
‘Yan kasar ta Lebanon, sun sha alwashin komawa kauyuka da garuruwansu, duk da barazanar da Isra’ila ke yi.
A karshen mako ne, sojojin Isra’ila suka gargadi al’ummar Lebanon da kada su koma garuruwansu na kudancin kasar.
Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hizbullah a ranar 27 ga watan Nuwamban 2024, bayan ta tafka asara mai yawa a fagen daga da kuma kasa cimma burinta duk da kashe mutane sama da 4,000 a Lebanon.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Iran ya sha alwashin inganta hadin gwiwa da Rasha
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi alkawarin kara bunkasa huldar Iran da Rasha ta hanyar kara kaimi wajen ga yarjejeniyoyin da ke tsakanin kasashen biyu da kuma ci gaba da mu’amala da cudanya mai ma’ana kan harkokin yankin.
A yayin ganawar da ya yi da ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov da ke ziyara a kasar, Pezeshkian ya bayyana dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da cewa tana kara habaka, tare da jaddada bukatar gaggauta aiwatar da yarjejeniyoyin da ke tsakaninsu, musamman ma cikakkiyar yarjejeniyar hadin gwiwa da ke tsakanin kasashen biyu.
Ya ce, “Iran da Rasha suna da rawar gani da za su iya takawa domin inganta hadin gwiwarsu, kuma mun kuduri aniyar karfafa huldar dake tsakanin Tehran da Moscow,” in ji shi.
Ya kuma jaddada muhimmancin ci gaba da yin cudanya mai ma’ana a tsakanin kasashen biyu.
Shugaban ya kara da cewa, “Iran da Rasha suna da ra’ayoyi iri-iri kan batutuwan da suka shafi yankin, kuma suna neman karfafa hadin gwiwarsu a matakai na kasa da kasa, ta hanyar huldar dake tsakaninsu, da kuma kungiyoyi irinsu kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai, da kungiyar Eurasia, da BRICS.”
Ministan na Rasha ya kuma jaddada cewa, za a yi duk mai yiwuwa don dorewa da kuma kara habaka wannan hadin gwiwa.
Lavrov ya ce, kammala shigar Iran cikin kungiyar tattalin arzikin Eurasia zai samar da wata sabuwar hanya mai inganci don karfafa dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu – musamman a fannin tattalin arziki da cinikayya.