An Tsawaita Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsakanin Isra’ila Da Lebanon Har Zuwa 18 Ga Watan Fabrairu
Published: 27th, January 2025 GMT
An tsawaita yarjejeniyar tsagaita bude wuta tsakanin Isra’ila da Lebanon na tsawon kimanin makonni uku bayan da gwamnatin kasar ta ki janye dakarunta kamar yadda aka kulla da farko.
An bayyana cewa yarjejeniyar tsakanin kasashen biyu za ta ci gaba da aiki har zuwa ranar 18 ga Fabrairu, 2025.
Shi ma firaministan kasar Labanon Najib Mikati ya tabbatar da tsawaita wa’adin, yana mai kara da cewa Lebanon za ta mutunta hakan.
Bisa yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka sanar tsakanin Isra’ila da Hizbullah a watan Nuwamba, a jiya ne ya kamata sojojin Isra’ila su fice daga kudancin Lebanon.
“Gwamnatin Lebanon ta sake jaddada aniyarta ta ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta har zuwa ranar 18 ga Fabrairu, 2025,” in ji Mikati a cikin wata sanarwa, a cewar kamfanin dillancin labarai na AFP.
Duk da haka a ranar Lahadi sojojin Isra’ila sun bude wuta kan al’ummar Lebanon da ke kokarin komawa gidajensu a kudancin kasar, inda suka kashe fararen hula akalla 22 tare da jikkata wasu fiye da 120 na daban.
‘Yan kasar ta Lebanon, sun sha alwashin komawa kauyuka da garuruwansu, duk da barazanar da Isra’ila ke yi.
A karshen mako ne, sojojin Isra’ila suka gargadi al’ummar Lebanon da kada su koma garuruwansu na kudancin kasar.
Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hizbullah a ranar 27 ga watan Nuwamban 2024, bayan ta tafka asara mai yawa a fagen daga da kuma kasa cimma burinta duk da kashe mutane sama da 4,000 a Lebanon.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Watan azumin Ramadana kan zo da sauye sauye da dama da suka haɗa da ƙara ƙaimi wajen bauta wa ubangiji, samun lada ta hanyar ciyar da al’umma da kuma falala masu yawa da ba su misaltuwa.
Wani sauyi da watan azumin watan Ramadana ke zuwa da shi shi ne canjin yanayin cimar al’umma, inda mutane ke canzawa daga cin abinci sau uku ko sama da haka a rana zuwa sahur da kuma buɗe-baki.
Bayan kwanaki 29 zuwa talatin na samun waɗannan canji, ta waɗanne hanyoyi ne al’umma za su koma cimaka kamar yadda suka saba gabanin watan Ramadana
NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Musulmi Su Yi Kafin Da Kuma Ranar Sallah DAGA LARABA: Yadda Farashin Kayan Masarufi Suke Gabanin SallahShirin Najeriya A Yau zai yi nazari ne kan hanyoyin da mutum ya kamata ya bi don komawa cin abinci yadda ya kamata bayan azumtar watan Ramadana.
Domin sauke shirin, latsa nan