HausaTv:
2025-03-02@20:19:08 GMT

Falasdinawan Da Sukayi Hijira Sun Fara Komawa Arewacin Gaza

Published: 27th, January 2025 GMT

Dubban daruruwan Falasdinawa da suka rasa matsugunansu sun fara komawa yankin arewacin zirin Gaza da yaki ya daidaita bayan da aka cimma matsaya tsakanin Hamas da Isra’ila.

Tuni kungiyar Hamas ta yaba da komawar Falasdinawan zuwa arewacin Gaza wanda ta danganta a abun tarihi.

An cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas bayan shafe watanni 15 ana gwabza kazamin yaki a Gaza.

An fara aiwatar da kashin farko na yarjejeniyar a ranar 19 ga watan Janairu, kuma ana sa ran za’a saki Falasdinawa sama da 1,890 da ‘yan Isra’ila 33, wadanda ke cikin 240 da kungiyoyin Hamas ta yi garkuwa dasu a harin ranar 7 ga watan Oktoban shekarar 2023.

Tun lokacin yakin ya lakume rayukan Falasdinawa akalla 47,306, akasari mata da kananan yara.

Kungiyar Hamas dai ta ce gwamnatin Isra’ila ta amince da tsagaita bude wuta bayan da ta gaza cimma wasu manufofinta na yakin.

Tun da farko dai, gwamnatin kasar ta ce Falasdinawa za su iya komawa arewacin kasar a ranar Litinin bayan da kungiyar gwagwarmayar Jihadin Islama ta Gaza ta tabbatar da cewa za a saki dan Isra’ila Arbel Yehud kafin a yi musanyan fursunoni na gaba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila

Shugabannin kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombia sun jaddada aniyarsu ta hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila amfani da tashar jiragen ruwansu, a daidai lokacin da gwamnatin kasar ke ci gaba da aiwatar da kisan kare dangi a zirin Gaza.

“Za mu hana jiragen ruwa da ke dauke da kayan aikin soji zuwa Isra’ila amfani da tashoshin jiragen ruwanmu; kamar yadda,” Shugaban Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, Firayim Ministan Malaysia Anwar Ibrahim da Shugaban Colombia Gustavo Petro suka rubuta a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da mujallar harkokin waje ta buga a wannan makon.

Sun jaddada cewa yakin da Isra’ila ke yi a Gaza ya fallasa gazawar tsarin kasa da kasa, tare da yin kira da a kawo karshen rashin hukunta dokokin kasa da kasa da Isra’ila ke yi.

Malesiya da Colombia na daga cikin kasashen da suka goyi bayan korafin kisan kiyashin da kasar Afrika ta kudu ta kai kan Isra’ila a kotun duniya ta ICJ.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas: Matakin Netanyahu na hana shigar kayan agaji a Gaza keta yarjejeniyar tsagaita wuta ne
  • Hamas Ta Bukaci Falasdinawa A Birnin Qudus Su Sabawa Dokar Takaita Yawan Masu Shiga Masallacin Al-Aksa A Kudus
  • Hamas Ta Yi Watsi Da Shawarar Isra’ila Na Tsawaita Matakin Farko Na Tsagaita Wuta A Gaza
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu
  • An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya 
  • An kori ma’aikatan Microsoft saboda adawa da yahudawan sahyoniya
  • An Fara Tattaunawa Tsakanin Isra’ila Da Hamas Kan Mataki Na Gaba Na Tsagaita Wuta
  • 7 Oktoba : Sojin Isra’ila Sun Amince Da “Cikakkiyar Gazawa” A Harin Hamas