Falasdinawan Da Sukayi Hijira Sun Fara Komawa Arewacin Gaza
Published: 27th, January 2025 GMT
Dubban daruruwan Falasdinawa da suka rasa matsugunansu sun fara komawa yankin arewacin zirin Gaza da yaki ya daidaita bayan da aka cimma matsaya tsakanin Hamas da Isra’ila.
Tuni kungiyar Hamas ta yaba da komawar Falasdinawan zuwa arewacin Gaza wanda ta danganta a abun tarihi.
An cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas bayan shafe watanni 15 ana gwabza kazamin yaki a Gaza.
An fara aiwatar da kashin farko na yarjejeniyar a ranar 19 ga watan Janairu, kuma ana sa ran za’a saki Falasdinawa sama da 1,890 da ‘yan Isra’ila 33, wadanda ke cikin 240 da kungiyoyin Hamas ta yi garkuwa dasu a harin ranar 7 ga watan Oktoban shekarar 2023.
Tun lokacin yakin ya lakume rayukan Falasdinawa akalla 47,306, akasari mata da kananan yara.
Kungiyar Hamas dai ta ce gwamnatin Isra’ila ta amince da tsagaita bude wuta bayan da ta gaza cimma wasu manufofinta na yakin.
Tun da farko dai, gwamnatin kasar ta ce Falasdinawa za su iya komawa arewacin kasar a ranar Litinin bayan da kungiyar gwagwarmayar Jihadin Islama ta Gaza ta tabbatar da cewa za a saki dan Isra’ila Arbel Yehud kafin a yi musanyan fursunoni na gaba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
ICC ta yi kakkausar suka ga Hungary saboda yin watsi da sammacin kama Netanyahu
Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC) mai hedkwata a birnin Hague ta yi Allah-wadai da matakin da kasar Hungary ta dauka na kin mutunta sammacin kame firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da zai ziyarci kasar da ke tsakiyar Turai a ranar Alhamis.
Mai magana da yawun kotun, Fadi El Abdallah, ya fada yayin wani taron manema labarai cewa, bai kamata mambobin kotun ICC su yi watsi da hukuncin kotun ba.
Kakakin ya ci gaba da cewa dole ne mambobin kotun su aiwatar da hukuncin da kotun ta yanke.
Ana sa ran Netanyahu zai isa Budapest a yammacin yau Laraba don ziyarar kwanaki hudu, bisa gayyatar Firaministan Hungary Viktor Orbán.
Shugaban na Hangari mai tsatsauran ra’ayi ya gayyaci takwaransa na Isra’ila duk da tuhumar da ake yi wa Netanyahu a hukumance da laifin amfani da yunwa a matsayin hanyar yaki da kuma aikata laifukan cin zarafin bil’adama a Gaza.
Kotun hukunta manyan laifuka ta ICC ta bayar da sammacin kama Netanyahu da tsohon ministansa na yaki, Yoav Gallant, bisa zargin laifukan yaki da cin zarafin bil adama a ranar 21 ga Nuwamba, 2024.
An bayar da sammacin ne bayan tantance akwai “kwararen dalilai ” dake cewa Netanyahu da Gallant “da gangan sun hana farar hula a Gaza abuban more rayuwa, ciki har da abinci, ruwa, da magunguna da kuma man fetur da wutar lantarki.” A Gaza.
A matsayinta na mamba a kotun hukunta manyan laifuka ta ICC, dole ne Hungary ta kama Netanyahu da zarar ya isa a tsakiyar nahiyar Turai tare da mika shi ga kotu, saidai duk da haka Hungary, ta fito karara cewa ba za ta mutunta hukunci da bukatun kotun ta ICC ba.