Aminiya:
2025-03-03@09:30:23 GMT

Ɗan shekara 30 ya mutu a kududdufi a Kano

Published: 27th, January 2025 GMT

Ana fargabar cewa wani mutum mai shekaru 30, Rabiu Sani, ya mutu a wani kududdufi da ke unguwar Kunture a Ƙaramar Hukumar Ungogo da ke Jihar Kano.

Mai magana da yawun rundunar hukumar kwana-kwana, Saminu Yusuf Abdullahi ne ya sanar da hakan a ranar Litinin.

’Yan majalisa sun nemi cin hancin N480m kafin amincewa da kasafin jami’o’i —Bincike NAJERIYA A YAU: Dabarun Bunƙasa Kasuwanci Ta Intanet

Ya bayyana cewa ofishin karɓar koken gaggawa ne ya samu kira daga wani Silas Munkhaila dangane da faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa jami’ansu sun isa kududdufin inda suka tsamo gawar mutumin wanda ya je ɗebo wa mahaifinsa ruwa.

Ya ƙara da cewa sun miƙa gawar mamacin a hannun mai unguwar Kunture, Uba Abdulkadir.

Kazalika, ya tabbatar da cewa tsautsayi da ba ya wuce ranarsa ne ya sanya mutumin zama ya faɗa rafin, lamarin da ya yi ajalinsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Rafi

এছাড়াও পড়ুন:

MDD Ta Bayyana Cewa Yara Fiye Da 100,000 Ne Suka Ka Yi Rijistan Fara Karatu A Makarantun Gaza Na Sabuwar Shekarar Karatu

Kakakin Majalisar dinkin MDD Stephane Dujarric ya bada sanarwan cewa yana makaranta a Gaza fiye da 100,000 suka fara karatu a makarantu a yankin a ranar 23 ga watan Fabrayrun da muke ciki.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jami’in MDD yana fadar haka a jiya Alhamis kwanaki huda da fara karatu a yankin na Gaza, bayan tsekon da aka samu saboda yakin da HKI ta dorawa kasar na tsawon shekara guda da watanni.

Dujarric ya bayyana cewa a halin yanzu makarantu 165 suka bude kofofin su ga yan makaranta a gaza, kuma ga mafi yawansu wannan shi ne karo na farko da suka shiga aji a cikin watanni 16 da suka gabata.

Jami’an gwamnati a Gaza sun bayyana cewa HKI ta rausa kashi 85% na makarantun Gaza a cikin yakin da ta dorawa yankin daga cikin watan Octoban shekara ta 2023.

Labarin ya kara da cewa akalla daliban makaran 12,800 da malaman makaranta  da ma’aikatan makarantu 800 suka rasa rayukansu a yankin na shekara guda da watanni. Sannan HKI ta rusa cibiyoyin karatu akalla 1,166 a wannan yakin. Banda haka yakin ya jawo asarar dalar Amurla billiyon $2 wa bangaren ilmintarwa a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɓacewar bindigogi 4,000: Sakaci ne dalili —’Yan sanda
  • Fasinjoji 12 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Edo
  • An kama ɓarayin waya a Kano
  • Shugabar Tanzaniya Ta Yaba Da Yadda Ake Ci Gaba Da Samun Karuwar Jigilar Kayayyaki A Tashar Tanga Da Sin Ta Inganta
  • ‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina
  • Bayan Kwana 22, Tsohon Shugaban NYSC Tsiga Ya Kuɓuta A Hannun Ƴan Bindiga
  • MDD Ta Bayyana Cewa Yara Fiye Da 100,000 Ne Suka Ka Yi Rijistan Fara Karatu A Makarantun Gaza Na Sabuwar Shekarar Karatu
  • Gwamnatin Sakkwato ta nemi malaman Jami’a su janye yajin aiki 
  • Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa
  • Gwamnatin Kano Ta Shirya Taron Bita Don Jami’an Watsa Labarai