Leadership News Hausa:
2025-03-31@15:32:01 GMT

‘Yan Bindiga Sun Sace Magidanci Da Iyalansa Da Makwabta A Abuja

Published: 27th, January 2025 GMT

‘Yan Bindiga Sun Sace Magidanci Da Iyalansa Da Makwabta A Abuja

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wani mutum da matarsa da dansa da wasu mutane biyu a Bwari da ke babban birnin tarayya, Abuja (FCT). LEADERSHIP ta tattaro cewa, an kai harin ne a unguwar Chikakore da ke Kubwa da misalin karfe 12 na safiyar ranar Litinin. Shugaba Xi Ya Yaba Da Ci Gaban Kasar Sin Duk Da Kalubalen Da Aka Fuskanta A Shekarar Dragon Tinubu Ya Isa Tanzania Don Halartar Taron Makon Makamashi Na Afrika  Majiyoyi sun ce, kimanin mahara 30 ne dauke da bindigogi kirar AK-47, suka kai hari gidan wani Mista Adefija Michael Akinropo, inda suka yi awon gaba da shi, da matarsa, da dansa, da kuma kanensa.

Bugu da kari, ‘yan bindigar sun afka makwabta kusa da wani gidan kiwon kaji, inda suka yi garkuwa da wani mutum tare da raunata matarsa ​​a yayin harin. Da aka tuntubi jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yansandan FCT, Josephine Adeh, ta bayyana cewa, za ta yi cikakken bayani bayan ta tattara bayanai kan lamarin.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo

’Yan Sanda sun kama mutum 14 da ake zargi da hannu a kisan matafiya 16 ’yan Arewa a kan titin Uromi zuwa Obajana, a Jihar Edo.

Sufeto-Janar na ’Yan Sanda (IGP), Kayode Egbetokun, ya yi tir da wannan hari, kuma ya bai wa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Hedikwatar Rundunar da ke Abuja, yin bincike.

Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a Abuja

Bayan faruwar lamarin, rundunar ’yan sandan Jihar Edo, ta tura jami’anta zuwa yankin domin wanzar da zaman lafiya.

Har ila yau, ana ci gaba da farautar sauran waɗanda suka tsere.

Kakakin rundunar ’yan sanda, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya ce Sufeto-Janar ya ba da umarnin a kamo waɗanda ke da hannu a lamarin.

Ya tabbatarwa da al’umma cewa ’yan sanda ba za su yarda da kisan gilla ba, kuma duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci.

Sufeto-Janar ya buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu kuma su ba da haɗin kai wajen bincike.

Haka kuma, ya gargaɗi mutane kan ɗaukar doka a hannunsu, tare da tunatar da su cewa mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba laifi ne.

’Yan sanda sun kuma gargaɗi jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu, tare da kiran su da su riƙa kai rahoton duk wani abu da suka gani wanda ba su yarda da shi ga hukumomin tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ‘Yan Banga A Edo Suka Yi Sanadin Kashe Matafiya Mafarauta 16 – Direban Motar
  • Gwarzon gasar Alƙur’ani ya Kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina
  • Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone
  • Girgizar ƙasa ta hallaka sama da mutum 1000 a Myanmar
  • Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo
  • An kashe mutum 10 a wani sabon hari a Filato
  • An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a Abuja
  • Tinubu Ya Ba Da Umarnin Kamo Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Girgizar ƙasa ta kashe mutum 150 a Myanmar da Thailand
  • An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara