HausaTv:
2025-03-01@02:10:08 GMT

Lebanon: Mutanen Kudancin Lebanon Suna Ci Gaba Da Kowama Garuruwansu

Published: 27th, January 2025 GMT

A rana ta biyu a jere, mutanen kudancin Lebanon suna ci gaba da komawa gururwansu da kauyukansu duk da hare-haren da Isra’ila take kai musu.

Tashar talabijin din “almayadin” mai watsa shirye-shiryenta daga kasar Lebanon ta ce, jirgin Isra’ila maras matuki,ya jefa bom din sauti na tsorata mutanen da suke komawa garuruwan nasu ,musamman a gefen garin Lamisul-Jabal, domin hana su shiga.

Mutanen garin sun ce za su shiga garin nasu ko da kuwa za su yi shahada ko kuma su jikkata.

Haka nan kuma sojojin na HKI sun kai farmaki akan sojojin Lebanon da suka taru a yankin al-Mafilah.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Lebanon ta sanar da cewa, mutane biyu sun jikkata sanadiyyar hare-haren na HKI a yau Litinin.

A jiya Lahadi ne dai wa’adin kwanaki 60 daga kare yakin Lebanon ya cika, da yarjejeniyarsa ta kunshi ficewar sojojin HKI daga garuruwan da su ka yi kutse.

Sai dai sojojin na mamaya sun ki ficewa, da hakan ya sa mutanen kudancin Lebanon su ka kutsa cikin garuruwan nasu. A kalla mutane 22 ne su ka yi shahada a jiya da kuma jikkata wasu masu yawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram: An lalata gidaje da makarantu a ƙauyukan Adamawa

Wasu gungun ‘yan Boko Haram ɗauke da muggan makamai sun kai farmaki cikin dare a garin Kwapre da ƙauyukan da ke gundumar New Yadul a ƙaramar hukumar Hong a Jihar Adamawa.

Harin wanda ya fara daga misalin ƙarfe 7:30 na yammacin ranar Talata, 25 ga watan Fabrairu, kuma ya ɓarnata dukiyoyi a tsakiyar daren.

Kotu ta yanke wa matashi ɗaurin wata 6 kan satar kaza Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90 a Borno

Al’ummar yankin sun ce, an ƙona wuraren ibada da makarantu da gidaje da wuraren kasuwanci, sannan an wawushe dukiyoyi na miliyoyin Naira.

Mista Joel Kulaha, Hakimin garin Kwapre da Abalis Jawaja, kuma dagacin ƙauyen, ya ce maharan sun farwa al’ummar garin, inda suka ƙona gine-gine tare da kwashe kayayyaki masu daraja.

Sun ce, an yi sa’a ba a rasa rayuka a harin ba, domin mazauna yankin sun yi gargaɗin ƙaruwar barazanar harin, sun tsere daga gidajensu kafin maharan su iso.

“Mun tsere da rayukanmu, amma duk abin da muka mallaka ya tafi,” kamar yadda Kulaha ya koka, yana kwatanta harin da aka kai.

An samu rahoton cewa dakarun sojin da ke kusa da Garaha sun mayar da martani kan harin da sanyin safiya, inda suka fatattaki maharan.

Sai dai mazauna yankin sun ce matakin sojan ya makara ne domin daƙile ɓarnar da ta ɓarke ƙauyukan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Masallacin Juma’a A Garin Samamiya Da Ke Birnin Kudu
  • An Yi Jana’izar Shahidan kungiyar Hizbullah Fiye Da 120 Kudancin Kasar Lebanon A Yau Jumma’a
  • Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu
  • LEADERSHIP HAUSA Ta Bayyana Wadanda Suka Yi Nasara A Gasar Gajerun Labaran Soyayya
  • Boko Haram: An lalata gidaje da makarantu a ƙauyukan Adamawa
  • Ɗangote Ya Rage Farashin Man Fetur Saboda Gabatowar Azumi
  • Sojojin Iran Sun Kammala Atisayen Zulfikar 1403 Da Faretin Sojojin Ruwa
  • Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno
  • Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Kudancin Syria
  • Nebenzia : Hare-haren Sojojin Isra’ila a Lebanon da Syria na kara dagula lamura a yankin