Dubban Falasdinawa Suna Ci Gaba Da Komawa Gidajensu Na Arewacin Gaza
Published: 27th, January 2025 GMT
A Yau Litinin ne dai da safe dubban Falasdinawa su ka fara komawa Arewacin Lebanon bayan gushewar watanni 15 na yaki.
Dubban Falasdinawan ne dai suke tafiya a kafa, yayin da wasu suke tafiya a cikin manyan motoci suna bi ta titin Salahuddin.
Tun da fari tashar talabijin din 12: ta HKI, ta watsa labarin cewa; sojoji sun janye daga mashigar Natsarim, da su ka kafa domin yin bincike tun ranar 27 ga watan Oktoba 2023.
Da dama daga cikin Falasdinawan sun kwana a wannan mashigar bayan da sojojin HKI su ka hana su wucewa a jiya Lahadi.
Barin Falasdinawan su koma arewacin Gaza, yana a karkashin yarjejeniyar da aka cimmawa a tsakaninsu da Hamas,dangane da fursunonin yaki.
A jiya Lahadi kasar Katar ta sanar da cewa an cimma matsaya a tsakanin bangarorin biyu da zai bayar da damar komawar Falasdinawan zuwa gidajensu a Arewacin Gaza.
A can HKI, kafafen watsa labaru suna daukar komawar Falasdinawan zuwa gidajensu dake Arewacin Gaza a matsayin koma baya ga Isra’ila. Isra’ilan dai ta so korar Falasdinawa ne baki daya daga Arewacin Gaza da hana su komawa, domin ta gina shigen tsaro, sai dai kuma hakarta ba ta cimma tura ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas ta yi watsi da shirin kwance damara na Isra’ila
Kungiyar Hamas ta yi watsi da kudirin baya bayan nan na Isra’ila na kwance damarar kungiyoyin gwagwarmayar Falasdinawa domin tsagaita bude wuta a Gaza, tana mai kiran hakan a matsayin wani yunkuri na gurgunta ‘yancin Falasdinu.
Tattaunawar da ake ci gaba da yi tsakanin Isra’ila da Hamas ta tsaya cik, inda Isra’ila ta matsa kaimi kan batun kwance damara, yayin da Hamas ta dage kan hakan a matsayin wani muhimmin hakki na kare Falasdinu.
Mahmoud Mardawi na kungiyar Hamas ya jaddada cewa kwance damarar kungiyoyin gwagwarmayar Falasdinawa abu ne da ba zai yiwu ba.
Ya bayyana kudurin na Isra’ila a matsayin wani dabarun yahudawan sahyoniya da Amurka na kwacewa Falasdinawa karfin kare kansu da kuma tinkarar mamaya.