Kungiyar “ISWAP” Ta Kashe Sojojin Najeriya 20
Published: 27th, January 2025 GMT
A kalla sojojin Najeriya 20 ne su ka kwanta dama daga cikinsu har da kwamanda a wani hari da ake dangantawa kungiyar ‘yan ta’adda ta ISWAP.
‘Yan ta’addar sun kai harin ne dai a ranar Juma’ar da ta gabata a kan sansanin bataliya ta 146 dake Malam-Fatori a akan iyakar Najeriya da Nijar a jihar Borno.
Wani soja da ya tsira daga wannan harin ya fadi cewa harin ‘yan ta’addar ya dauki sa’oi 3, kuma sun je wurin ne a cikin manyan motoci tare da shammatar sojojin.
Kamfanin dillancin labarun Reuters wanda ya ambato sojan ya ce, maharan sun rika harbinsu ta kowace kusurwa, sai dai sun mayar da wuta.Haka nan kuma ya tabbatar da cewa an kashe kwamandnsu.
Mazaunan yankin da aka kai harin sun tabbatar da cewa maharan sun kone gine-gine masu yawa, da ya tilastawa mazauna yankin yin hijira.
Haka nan kuma an tabbatar da cewa har zuwa Asabar da dare an rika ganin maharan a cikin wannan yankin suka karakaina.
Ita dai kungiyar “ISWAP” ta balle ne daga Bokoharam a 2016, kuma tana kai wa sojoji da jami’an tsaron Najeriya hare-hare. A tsawon shekaru 15 na hare-haren ‘yan ta’adda a wannan yankin mutane kusan 40,000 ne su ka kwanta dama,wasu miliyan biyu kuwa su ka tarwatse.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Halin Da Matasa Suka Tsinci Kansu A Najeriya
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
A yau, da dama daga cikin matasan Najeriya na fama da matsaloli masu tarin yawa, musamman wajen ciyar da kansu da biyan buƙatunsu na yau da kullum.
Wannan na faruwa ne sakamakon halin da tattalin arziƙin ƙasa ke ciki, rashin aikin yi, da kuma tsadar rayuwa.
NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye NAJERIYA A YAU: Illar Sare Itatuwa Ga Sauyin Yanayi Da LafiyarmuWasu daga cikin matasan sun kammala karatu, wasu kuma suna da sana’o’in hannu, amma duk da haka, rashin samun aikin da zai biya musu buƙatunsu yana ƙara jefa su cikin mawuyacin hali.
Wannan matsala na ci gaba da haddasa damuwa ga matasan ƙasar, inda da dama daga cikinsu ke fuskantar ƙuncin rayuwa sakamakon rashin tabbas a makomarsu.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana, zai nazarci irin waɗannan ƙalubale da matasa ke fuskanta, musamman a matakin farko na rayuwarsu.
Domin sauke shirin, latsa nan